• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turai Ta San Ra’ayin Amurka Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Turai Ta San Ra’ayin Amurka Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya ne, shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya gama ziyararsa ta kwanaki 3 a kasar Amurka. Shugaba Macron ya ziyarci Amurka a wannan karo don sa kaimi ga kasar Amurka da ta gyara dokar rage hauhawar farashin kaya bisa la’akari da kamfanonin Turai.

Amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba, inda ya koma Turai ta bacin rai, duk da dangantakar dake tsakanin Turai da Amurkar.

  • Ma’aikatar Tsaron Amurka Ta Fitar Da Rahoton Shekara-Shekara Kan Karfin Sojan Sin Da Nufin Fakewa Wajen Nuna Danniya Ko Babakere A Fannin Soja

Shugaba Macron ya ziyarci Amurka a wannan karo don neman dawo da moriyar Turai. A watan Agusta na bana, shugaban kasar Amurka Joseph Biden, ya sa hannu kan dokar rage hauhawar farashin kaya, inda aka gabatar da matakai da dama, ciki har da samar da kudin rangwame don sa kaimi ga kamfanonin da ke kasar Amurka da su raya fasahohin kera motoci masu amfani da wutar lantarki da sauran fasahohi ba tare da gurbata muhalli ba.

Kasashen Turai sun nuna rashin jin dadi da wannan doka, domin a ganinsu, dokar tana kunshe da abubuwan bada kariya ga cinikayya, wadda ta sabawa ka’idojin hukumar WTO, kuma hakan zai tsananta halin da masana’antun samar da kaya na Turai ke game da game da kokarinsu na samar da kayayyaki, da tilastawa rassan kamfanonin Turai kaura zuwa kasar Amurka.

Yayin da shugaba Macron ya isa kasar Amurka a yini na farko, ya fara zargin babbar illar da dokar rage hauhawar farashin kaya ta Amurka ta haifar wa kamfanonin Turai, ya ce za a rasa ayyukan yi da dama a kasar Faransa da ma nahiyar Turai, kuma an dauki matakin ne don daidaita matsalar Amurka tare da kawo illa ga moriyar Turai. Shugaba Macron ya kara da cewa, kasar Faransa tana fatan kasar Amurka za ta dauki Faransa a matsayin abokiya, tare da kara yin mu’amala da juna kan tattalin arziki a tsakanin gabobin tekun Atlantic.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Game da bukatun da shugaba Macron ya gabatar, shugaba Biden ya ce kasar Amurka ba ta bukatar yin afuwa ga nahiyar Turai, Amurka za ta dan yiwa dokar gyara ne, amma bai yi karin haske ba. Kafofin watsa labarai na kasar Jamus sun bayyana cewa, game da batun moriyar tattalin arziki, kasar Amurka tana kula da moriyarta ce kawai, don haka ya kamata kasashen Turai su san da haka. (Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Markus Ya Shaki Iskar ‘Yanci Daga Hannun Masu Garkuwa Bayan Shafe Kwanaki 14

Next Post

Kumbon Shenzhou-14 Ya Sauka Cikin Nasara

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

11 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

12 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

13 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

14 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

15 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Kumbon Shenzhou-14 Ya Sauka Cikin Nasara

Kumbon Shenzhou-14 Ya Sauka Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.