ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turai Ta San Ra’ayin Amurka Kan Dangantakar Dake Tsakaninsu

by CMG Hausa
4 years ago
Amurka

A kwanakin baya ne, shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya gama ziyararsa ta kwanaki 3 a kasar Amurka. Shugaba Macron ya ziyarci Amurka a wannan karo don sa kaimi ga kasar Amurka da ta gyara dokar rage hauhawar farashin kaya bisa la’akari da kamfanonin Turai.

Amma hakarsa ba ta cimma ruwa ba, inda ya koma Turai ta bacin rai, duk da dangantakar dake tsakanin Turai da Amurkar.

  • Ma’aikatar Tsaron Amurka Ta Fitar Da Rahoton Shekara-Shekara Kan Karfin Sojan Sin Da Nufin Fakewa Wajen Nuna Danniya Ko Babakere A Fannin Soja

Shugaba Macron ya ziyarci Amurka a wannan karo don neman dawo da moriyar Turai. A watan Agusta na bana, shugaban kasar Amurka Joseph Biden, ya sa hannu kan dokar rage hauhawar farashin kaya, inda aka gabatar da matakai da dama, ciki har da samar da kudin rangwame don sa kaimi ga kamfanonin da ke kasar Amurka da su raya fasahohin kera motoci masu amfani da wutar lantarki da sauran fasahohi ba tare da gurbata muhalli ba.

ADVERTISEMENT

Kasashen Turai sun nuna rashin jin dadi da wannan doka, domin a ganinsu, dokar tana kunshe da abubuwan bada kariya ga cinikayya, wadda ta sabawa ka’idojin hukumar WTO, kuma hakan zai tsananta halin da masana’antun samar da kaya na Turai ke game da game da kokarinsu na samar da kayayyaki, da tilastawa rassan kamfanonin Turai kaura zuwa kasar Amurka.

Yayin da shugaba Macron ya isa kasar Amurka a yini na farko, ya fara zargin babbar illar da dokar rage hauhawar farashin kaya ta Amurka ta haifar wa kamfanonin Turai, ya ce za a rasa ayyukan yi da dama a kasar Faransa da ma nahiyar Turai, kuma an dauki matakin ne don daidaita matsalar Amurka tare da kawo illa ga moriyar Turai. Shugaba Macron ya kara da cewa, kasar Faransa tana fatan kasar Amurka za ta dauki Faransa a matsayin abokiya, tare da kara yin mu’amala da juna kan tattalin arziki a tsakanin gabobin tekun Atlantic.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Game da bukatun da shugaba Macron ya gabatar, shugaba Biden ya ce kasar Amurka ba ta bukatar yin afuwa ga nahiyar Turai, Amurka za ta dan yiwa dokar gyara ne, amma bai yi karin haske ba. Kafofin watsa labarai na kasar Jamus sun bayyana cewa, game da batun moriyar tattalin arziki, kasar Amurka tana kula da moriyarta ce kawai, don haka ya kamata kasashen Turai su san da haka. (Zainab)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Kumbon Shenzhou-14 Ya Sauka Cikin Nasara

Kumbon Shenzhou-14 Ya Sauka Cikin Nasara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.