Tawagar Super Eagles za ta buga wasan karshe na kofin sada zumunta na Unity Cup tsakaninta da kasar Jamaica a filin wasa na Gtech dake birnin Landan a yau Asabar da misalin karfe 5 agogon Nijeriya.
Nijeriya ta doke kasar Ghana da ci 2-1 a wasan farko wanda ya bata damar zuwa wannan matakin, kamar yadda Jamaica ta doke Trinidad And Tobago a wasan farko da ci 3-2.
- Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo
- Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu
Duka kasashen biyu na fatan ganin sun samu nasara a wasan, wanda zai iya kasancewa wata alama ta yadda kasashen ke shirya wa tunkarar wasannin neman gurbi a gasar kofin Duniya da za a buga a kasashen Amurka, Canada da Mexico.
Kyaftin din tawagar Super Eagles Ahmed Musa kamar yadda Leadership Hausa ta ruwaito tunda farko, ya bar sansanin tawagar dake Landan inda ya dawo gida Nijeriya domin halartar daurin aurensa da akayi ranar Juma’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp