• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Raba Babura 42 Da Motoci 2 Domin Inganta Sa ido Kan Cutar Tarin Fuka

byUmar Faruk
1 year ago
Kebbi

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, ta raba babura 42 da motoci kirar Hilux guda biyu ga jami’an sa ido ga masu fama da cutar tarin fuka a jihar.

Asusun Tallafawa Duniya ne ya bayar da tallafin motocin yaki da cutar AIDS, tarin fuka da zazzabin cizon sauro (GFATM) a matsayin gudunmuwarsu kan yakin da wadannan cututtukan a duk fadin Jihar Kebbi.

  • ‘Yancin Kai: PDP Ta Bukaci Tinubu Ya Rage Kudin Man Fetur
  • Gwamnatin Kaduna Ta Raba Wa Manoma Taki Buhu 120,000 

A wajen bikin, Hajiya Zainab ta bayyana muhimmancin kara kaimi wajen yaki da cutar tarin fuka a jihar.

Ta bayyana bukatar karfafa sa ido, musamman a yankunan da ke da wuyar isa, don tabbatar da cewa ba a bar kowa a baya ba wajen yaki da cutar tarin fuka.

“Wadannan motocin za su inganta zirga-zirgar ma’aikatan kiwon lafiya, da ba su damar isa yankunan da ke nesa, da gano masu cutar tarin fuka a baya, da kuma samar da hanyoyin da suka dace,” in ji ta.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

“Dole ne mu ci gaba da wayar da kan jama’a game da alamun cutar tarin fuka da magani, rage kyama, da tabbatar da samun damar yin gwaji da ba da magani a kyauta.”

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta wallafa rahoton cewa cutar tarin fuka ta kasance babbar damuwa ga lafiyar jama’a.

Ta ce akalla mutane miliyan 2.5 ne suka kamu da cutar tarin fuka a yankin Afirka a 2022.

Shirin na WHO ya kawo karshen cutar tarin fuka yana da nufin rage tarin fuka da kashi 90% sannan sabbin masu kamuwa da cutar da kashi 80 cikin dari nan da shekarar 2030.

Dokta Moses Onoh, jami’in fasaha kan cutar tarin fuka a WHO, ya yaba wa kokarin Hajiya Zainab, ya kuma shawarci jami’an da su yi amfani da motocin yadda ya kamata.

Kwamishinan lafiya na jihar, Comrade Yunusa Musa Isma’il ya yabawa masu hannu da shuni da kuma uwargidan Gwamnan Jihar bisa wannan tallafi da suka bayar.

Wannan shiri ya nuna jajircewar Jihar Kebbi wajen yaki da cutar tarin fuka da kuma tabbatar da ingantaccen kiwon lafiya ga ‘yan jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
NUJ Ta Taya Gwamnan Kebbi Da Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai

NUJ Ta Taya Gwamnan Kebbi Da Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun 'Yancin Kai

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version