ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yancin Kai: PDP Ta Bukaci Tinubu Ya Rage Kudin Man Fetur

by Sadiq
2 years ago
PDP

Jam’iyyar adawa ta PDP, ta bukaci jam’iyyar APC da ta sauya akalar tsare-tsaren da suke kuntata wa al’umar kasar nan.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a game da samun ‘yancin kasa, dauke da sa hannun kakakinta, Debo Ologunagba, PDP ta ce APC ta yi wa ‘yan Nijeriya alkawura da dama wadanda ba ta cika ba.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Raba Wa Manoma Taki Buhu 120,000 
  • Kauyen Yugonglou Da Ya Shaida Bunkasuwar Kauyukan Kasar Sin

Daga cikin kiran da jam’iyyar adawar ta yi har da batun rage kudin man fetur da aka kara a farkon watan Satumba.

ADVERTISEMENT

“Ya kamata ba tare da bata lokaci ba, Gwamnatin Tarayya ta rage farashin man fetur da kuma dakile faduwar darajar Naira ta hanyar sake tsara albarkatu domin farfado da sashen samar da kayayyaki da ke tangal-tangal.”

“Akwai bukatar APC ta fahimci cewa Nijeriya kasa ce mai ‘yancin kai kuma mulki yana hannun mutane.”

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

“Saboda haka, ya zama dole gwamnati karkashin jagorancin APC ta saurari ‘yan Nijeriya ta sake duba dukkanin manufofi da ayyukan da ba sa amfanar da jama’a wadanda ke takura rayuwa a kasar nan,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, “hakika, ‘yan Nijeriya suna cikin radadi! dole ne a dauki mataki yanzu ta hanyar karkatar da albarkatu zuwa ayyukan da ke da tasiri kai tsaye ga jin dadin ‘yan Nijeriya.”

A baya, shugaban kasa Bola Tinubu ya sha bayyana dalilan da suka sa aka cire tallafin man fetur.

A cewar Tinubu ‘yan Nijeriya sun fi amfana da cire tallafin mai duk da cewa rahotanni na nuni da akasin hakan duba da yadda kayayyaki ke tashin gwauron zabi.

Dangane da karin kudin mai da aka yi a baya-bayan nan, Tinubu ya ce wannan hurumi ne na kamfanin mai na kasa (NNPCL), wanda ya ce ana binsa biliyoyin kudi a matsayin bashi.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Raba Babura 42 Da Motoci 2 Domin Inganta Sa ido Kan Cutar Tarin Fuka

Uwargidan Gwamnan Kebbi Ta Raba Babura 42 Da Motoci 2 Domin Inganta Sa ido Kan Cutar Tarin Fuka

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.