• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Ke Da Gaskiya Tsakanin NDLEA Da Sanata Ashiru? 

by Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
Wa Ke Da Gaskiya Tsakanin NDLEA Da Sanata Ashiru? 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Nijeriya (NDLEA) ta ce, dan majalisa daga Jihar Kwara kuma mataimakin shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Oyeyola Ashiru, ya farmaki ayyukanta ne saboda kwato wasu miyagun kwayoyi a gidansa.  

A yayin zaman majalisar na ranar 15 ga Octoba, dan majalisar ya ce, “NDLEA ta kasance hukuma mai cin hanci da rashawa.” don haka ya yi kira da a samar da wata sabowar hukumar da za dunga yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi.

  • Abin Da Ya Sa Ƙasashen Duniya Suka Gina Majalisar Ɗinkin Duniya – Sakatare Janar
  • Super Eagles Ta Hauro Matsayi Na 36 A Jadawalin Duniya Na FIFA

Ya yi kiran ne a kan kudurin neman kafa cibiyar wayar da kai kan ta’ammuli da kwayoyi da gyaran hali ta kasa.

Sai dai bayan furucin nasa, NDLEA ta mayar da zazzafan martani a gareshi.

Shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa ya ce, fushin da sanatan ya yi ya fito ne sakamakon kullin da ke ransa kuma babu kanshin gaskiya a lamarin.

Labarai Masu Nasaba

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Da yake ganawa da ‘yan jarida ta bakin kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya ce NDLEA ta dukufa wajen gudanar da ayyukan da suke kanta na dakile sha da fataucin miyagun kwayoyi ciki kuwa har da wani kame da ta yi a gidan sanatan.

Babafemi ya ce hukumar ta jira na tsawon mako guda domin dan majalisar ya fayyace matsayar kan wannan zargi da kazafin.

Ya ce, dole ne a garesu su fito su fayyace zare da abawa kan furucin sanatan, “Tabbas ba shakka kafa wata hukuma na wuyan majalisa, amma in an gayyacemu domin mu bayar da namu gudunmawar za mu bayar, za mu bayyana matsayarmu.”

Sai dai ya ce ba kuma za su zura ido wani sanata ya fito ya yi ta sharara batun da babu tushe a kansu ba kuma su yi shiru da bakinsu.

Ya bayar da labarin yadda aka yi sanatan ya fara fushi da su, “Kwanakin baya a wani gidan sanatan da ke GRA Ilorin a Jihar Kwara, mun kamo miyagun kwayoyi tare da kama wasu mukarraban sanatan su biyu, Ibrahim Mohammed da Muhammed Yahaya.

“Bisa bayanan sirri da muka samu ya tabbatar mana cewa gidan sanatan ya kasance wata dandamalin hada-hadar miyagun kwayoyi a tsakanin dillalai da masu amfani da shi. Don haka ne jami’anmu suka yi dirar mikiya a gidan da karfe 1:30 na dare a ranar 4 ga watan Fabrairun 2024, inda muka kama hadiminsa biyu, dayan na ukun kuma ya ari na kare,” Babafemi ya shaida.

Ya ce ba a nan ma rigimar tasu ta tsaya ba, “A wani takun tsaka da sanatan, hukumar ta kuma amshi wani rahoton sirri da ke cewa wasu yaran sanatan da aka fi sani da ‘Omo Senator’ wadanda suke amfani da gudanar da ayyukansu daga yankinsa, Offa, su ma suna hada-hadar miyagun kwayoyi. Mun kai samame a wata mahadarsu da ke Offa, inda daya daga cikinsu Oluwatosin Odepidan ya shiga hannu tare da miyagun kwayoyi a ranar 11 ga Yunin 2023.”

Sai dai jami’ar watsa labarai na sanatan, Hauwa Ahmad ta nuna takaicinsa kan irin zargin da hukumar ke yi wa sanatan. Ya ce, Sanata Ashiru na da ikon bayar da gudunmawar kan kowace kuduri da ke gaban majalisar. Don haka ta nuna cewa ya nemi a kafa wata hukuma bai dace NDLEA ta fusata ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AshiruNDLEASanata
ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Ya Ƙi Amince Wa Da Umarnin Majalisa Kan Dakatar Da Amfani Da Tsofaffin Naira

Next Post

Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

Related

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

8 minutes ago
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
Labarai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

4 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

5 hours ago
Tinubu
Labarai

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

6 hours ago
jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

19 hours ago
Next Post
Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

Hatsarin Jirgi Ya Sa Mataimakin Shugaban Kasa Ya Soke Ziyarar Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

June 14, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

June 14, 2025
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

June 14, 2025
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

June 14, 2025
Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

June 14, 2025
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

June 14, 2025
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

June 14, 2025
Tinubu

Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa

June 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci

June 14, 2025
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.