• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Gudunmawa Sin Za Ta Iya Bayarwa Ga Zaman Lafiyar Yankin Gabas Ta Tsakiya?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wacce Gudunmawa Sin Za Ta Iya Bayarwa Ga Zaman Lafiyar Yankin Gabas Ta Tsakiya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin nan, an shiga zullumi a duniya dangane da yanayin da ake ciki da kuma abun da gaba za ta haifar game da rikicin Isra’ila da Falasdinu da a yanzu ya shafi kasar Iran. Kuma dangane da hakan ne, a jiya aka tattauna ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Sin Wang Yi da takwarorinsa na Iran da Saudiyya.

Mun riga mun san cewa, kasar Sin ta samarwa kanta martaba da mutunci a idon duniya ta hanyar huldar mutunta juna da kuma cimma moriyar juna da kaucewa katsalandan da take aiwatarwa tsakaninta da kasa da kasa. Haka kuma, ko da yaushe, ta kasance mai kira da zaman lafiya da tattaunawa, maimakon nuna bangaranci ko ingiza rikici.

  • Sin Na Cikin Kasashe Mafiya Tsaro A Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Tun bayan barkewar wannan rikici, kasar Sin ta yi ta kada kuri’ar goyon bayan kudurorin Kwamitin Sulhu domin tsagaita bude wuta ba tare da sharadi ba, tare da tuntubar bangarori masu ruwa da tsaki da zummar shawo kan rikicin.

Matsayin kasar Sin da kimarta ka iya taka rawa wajen ganin tankiyar dake tsakanin Isra’ila da Iran bai ta’azzara ba. Kamar yadda Wang Yi ya fada a tattaunawarsa da takwaransa na Iran Hossein Amir-Abdollahian, hari kan ofishin jakadancin Iran a Damascus, take dokokin kasa da kasa ne, amma kuma Iran za ta iya tafiyar da lamarin yadda ya kamata, tare da kiyaye zaman lafiya a yankin. Idan muka duba wannan matsayin na Sin, za mu gane cewa, sanin ya kamata irin nata bai sa ta rura wutar rikicin ko zuga Iran ta ci gaba da kai hare-hare ko ingiza yaki ba. Maimakon haka, ta nuna wa Iran cewa za ta iya shawo kan matsalar ba tare da ta’azzara yanayin da yankin ke ciki ba. Wannan shi ne abun da ya kamata kasa da kasa su yi, musamam masu karfin fada a ji.

Baya ga haka, a tattaunawar Wang Yi da takwaransa na Saudiyya Faisal bin Farhan Al Saud, Saudiyya ta ce tana sa ran ganin Sin ta taka rawa wajen samun zaman lafiya a yankin, kuma a shirye take ta hada hannu da Sin wajen cimma hakan. Saudiyya muhimmiya ce a yankin Gabas ta Tsakiya kuma neman goyon bayan Sin da ta yi, ya nuna cewa, ta aminta da Sin din, haka kuma ta yarda da yunkuri da shawarwarinta game da batun da ma rawar da take takawa a harkokin da suka shafi kasa da kasa a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

A kullum, na kan bada misali da yanayin yawan al’umma da mabanbantan kabilu da ma mabiya addinai da Sin take da su da kuma zaman lafiya da ci gaban da suke morewa a kasar a matsayin abun koyi a duniya. Wadannan abubuwa da na zayyana, sun nuna karfi da gogewar Sin a harkokin da suka shafi tabbatar da zaman lafiya ba tare da zubar da jini ko tashin hankali ba. Haka kuma sun nuna cewa za ta iya taka rawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Garkuwa Da ‘Yan Makaranta: Nijeriya Ba Za Ta Sake Biyan Kuɗin Fansa Ba – Tinubu

Next Post

Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Related

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

3 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

4 hours ago
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

15 hours ago
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci
Daga Birnin Sin

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

16 hours ago
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

18 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

19 hours ago
Next Post
Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Mun Damu Da Matsalar Yara 'Yan Shila A Adamawa - Fintiri

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.