ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Gudunmawa Sin Za Ta Iya Bayarwa Ga Zaman Lafiyar Yankin Gabas Ta Tsakiya?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A ’yan kwanakin nan, an shiga zullumi a duniya dangane da yanayin da ake ciki da kuma abun da gaba za ta haifar game da rikicin Isra’ila da Falasdinu da a yanzu ya shafi kasar Iran. Kuma dangane da hakan ne, a jiya aka tattauna ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Sin Wang Yi da takwarorinsa na Iran da Saudiyya.

Mun riga mun san cewa, kasar Sin ta samarwa kanta martaba da mutunci a idon duniya ta hanyar huldar mutunta juna da kuma cimma moriyar juna da kaucewa katsalandan da take aiwatarwa tsakaninta da kasa da kasa. Haka kuma, ko da yaushe, ta kasance mai kira da zaman lafiya da tattaunawa, maimakon nuna bangaranci ko ingiza rikici.

  • Sin Na Cikin Kasashe Mafiya Tsaro A Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Tun bayan barkewar wannan rikici, kasar Sin ta yi ta kada kuri’ar goyon bayan kudurorin Kwamitin Sulhu domin tsagaita bude wuta ba tare da sharadi ba, tare da tuntubar bangarori masu ruwa da tsaki da zummar shawo kan rikicin.

ADVERTISEMENT

Matsayin kasar Sin da kimarta ka iya taka rawa wajen ganin tankiyar dake tsakanin Isra’ila da Iran bai ta’azzara ba. Kamar yadda Wang Yi ya fada a tattaunawarsa da takwaransa na Iran Hossein Amir-Abdollahian, hari kan ofishin jakadancin Iran a Damascus, take dokokin kasa da kasa ne, amma kuma Iran za ta iya tafiyar da lamarin yadda ya kamata, tare da kiyaye zaman lafiya a yankin. Idan muka duba wannan matsayin na Sin, za mu gane cewa, sanin ya kamata irin nata bai sa ta rura wutar rikicin ko zuga Iran ta ci gaba da kai hare-hare ko ingiza yaki ba. Maimakon haka, ta nuna wa Iran cewa za ta iya shawo kan matsalar ba tare da ta’azzara yanayin da yankin ke ciki ba. Wannan shi ne abun da ya kamata kasa da kasa su yi, musamam masu karfin fada a ji.

Baya ga haka, a tattaunawar Wang Yi da takwaransa na Saudiyya Faisal bin Farhan Al Saud, Saudiyya ta ce tana sa ran ganin Sin ta taka rawa wajen samun zaman lafiya a yankin, kuma a shirye take ta hada hannu da Sin wajen cimma hakan. Saudiyya muhimmiya ce a yankin Gabas ta Tsakiya kuma neman goyon bayan Sin da ta yi, ya nuna cewa, ta aminta da Sin din, haka kuma ta yarda da yunkuri da shawarwarinta game da batun da ma rawar da take takawa a harkokin da suka shafi kasa da kasa a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

A kullum, na kan bada misali da yanayin yawan al’umma da mabanbantan kabilu da ma mabiya addinai da Sin take da su da kuma zaman lafiya da ci gaban da suke morewa a kasar a matsayin abun koyi a duniya. Wadannan abubuwa da na zayyana, sun nuna karfi da gogewar Sin a harkokin da suka shafi tabbatar da zaman lafiya ba tare da zubar da jini ko tashin hankali ba. Haka kuma sun nuna cewa za ta iya taka rawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia
Daga Birnin Sin

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Next Post
Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Mun Damu Da Matsalar Yara 'Yan Shila A Adamawa - Fintiri

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.