ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Gudunmawa Sin Za Ta Iya Bayarwa Ga Zaman Lafiyar Yankin Gabas Ta Tsakiya?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A ’yan kwanakin nan, an shiga zullumi a duniya dangane da yanayin da ake ciki da kuma abun da gaba za ta haifar game da rikicin Isra’ila da Falasdinu da a yanzu ya shafi kasar Iran. Kuma dangane da hakan ne, a jiya aka tattauna ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Sin Wang Yi da takwarorinsa na Iran da Saudiyya.

Mun riga mun san cewa, kasar Sin ta samarwa kanta martaba da mutunci a idon duniya ta hanyar huldar mutunta juna da kuma cimma moriyar juna da kaucewa katsalandan da take aiwatarwa tsakaninta da kasa da kasa. Haka kuma, ko da yaushe, ta kasance mai kira da zaman lafiya da tattaunawa, maimakon nuna bangaranci ko ingiza rikici.

  • Sin Na Cikin Kasashe Mafiya Tsaro A Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Tun bayan barkewar wannan rikici, kasar Sin ta yi ta kada kuri’ar goyon bayan kudurorin Kwamitin Sulhu domin tsagaita bude wuta ba tare da sharadi ba, tare da tuntubar bangarori masu ruwa da tsaki da zummar shawo kan rikicin.

ADVERTISEMENT

Matsayin kasar Sin da kimarta ka iya taka rawa wajen ganin tankiyar dake tsakanin Isra’ila da Iran bai ta’azzara ba. Kamar yadda Wang Yi ya fada a tattaunawarsa da takwaransa na Iran Hossein Amir-Abdollahian, hari kan ofishin jakadancin Iran a Damascus, take dokokin kasa da kasa ne, amma kuma Iran za ta iya tafiyar da lamarin yadda ya kamata, tare da kiyaye zaman lafiya a yankin. Idan muka duba wannan matsayin na Sin, za mu gane cewa, sanin ya kamata irin nata bai sa ta rura wutar rikicin ko zuga Iran ta ci gaba da kai hare-hare ko ingiza yaki ba. Maimakon haka, ta nuna wa Iran cewa za ta iya shawo kan matsalar ba tare da ta’azzara yanayin da yankin ke ciki ba. Wannan shi ne abun da ya kamata kasa da kasa su yi, musamam masu karfin fada a ji.

Baya ga haka, a tattaunawar Wang Yi da takwaransa na Saudiyya Faisal bin Farhan Al Saud, Saudiyya ta ce tana sa ran ganin Sin ta taka rawa wajen samun zaman lafiya a yankin, kuma a shirye take ta hada hannu da Sin wajen cimma hakan. Saudiyya muhimmiya ce a yankin Gabas ta Tsakiya kuma neman goyon bayan Sin da ta yi, ya nuna cewa, ta aminta da Sin din, haka kuma ta yarda da yunkuri da shawarwarinta game da batun da ma rawar da take takawa a harkokin da suka shafi kasa da kasa a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A kullum, na kan bada misali da yanayin yawan al’umma da mabanbantan kabilu da ma mabiya addinai da Sin take da su da kuma zaman lafiya da ci gaban da suke morewa a kasar a matsayin abun koyi a duniya. Wadannan abubuwa da na zayyana, sun nuna karfi da gogewar Sin a harkokin da suka shafi tabbatar da zaman lafiya ba tare da zubar da jini ko tashin hankali ba. Haka kuma sun nuna cewa za ta iya taka rawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Mun Damu Da Matsalar Yara 'Yan Shila A Adamawa - Fintiri

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.