ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Gudunmawa Sin Za Ta Iya Bayarwa Ga Zaman Lafiyar Yankin Gabas Ta Tsakiya?

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A ’yan kwanakin nan, an shiga zullumi a duniya dangane da yanayin da ake ciki da kuma abun da gaba za ta haifar game da rikicin Isra’ila da Falasdinu da a yanzu ya shafi kasar Iran. Kuma dangane da hakan ne, a jiya aka tattauna ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Sin Wang Yi da takwarorinsa na Iran da Saudiyya.

Mun riga mun san cewa, kasar Sin ta samarwa kanta martaba da mutunci a idon duniya ta hanyar huldar mutunta juna da kuma cimma moriyar juna da kaucewa katsalandan da take aiwatarwa tsakaninta da kasa da kasa. Haka kuma, ko da yaushe, ta kasance mai kira da zaman lafiya da tattaunawa, maimakon nuna bangaranci ko ingiza rikici.

  • Sin Na Cikin Kasashe Mafiya Tsaro A Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Tun bayan barkewar wannan rikici, kasar Sin ta yi ta kada kuri’ar goyon bayan kudurorin Kwamitin Sulhu domin tsagaita bude wuta ba tare da sharadi ba, tare da tuntubar bangarori masu ruwa da tsaki da zummar shawo kan rikicin.

ADVERTISEMENT

Matsayin kasar Sin da kimarta ka iya taka rawa wajen ganin tankiyar dake tsakanin Isra’ila da Iran bai ta’azzara ba. Kamar yadda Wang Yi ya fada a tattaunawarsa da takwaransa na Iran Hossein Amir-Abdollahian, hari kan ofishin jakadancin Iran a Damascus, take dokokin kasa da kasa ne, amma kuma Iran za ta iya tafiyar da lamarin yadda ya kamata, tare da kiyaye zaman lafiya a yankin. Idan muka duba wannan matsayin na Sin, za mu gane cewa, sanin ya kamata irin nata bai sa ta rura wutar rikicin ko zuga Iran ta ci gaba da kai hare-hare ko ingiza yaki ba. Maimakon haka, ta nuna wa Iran cewa za ta iya shawo kan matsalar ba tare da ta’azzara yanayin da yankin ke ciki ba. Wannan shi ne abun da ya kamata kasa da kasa su yi, musamam masu karfin fada a ji.

Baya ga haka, a tattaunawar Wang Yi da takwaransa na Saudiyya Faisal bin Farhan Al Saud, Saudiyya ta ce tana sa ran ganin Sin ta taka rawa wajen samun zaman lafiya a yankin, kuma a shirye take ta hada hannu da Sin wajen cimma hakan. Saudiyya muhimmiya ce a yankin Gabas ta Tsakiya kuma neman goyon bayan Sin da ta yi, ya nuna cewa, ta aminta da Sin din, haka kuma ta yarda da yunkuri da shawarwarinta game da batun da ma rawar da take takawa a harkokin da suka shafi kasa da kasa a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A kullum, na kan bada misali da yanayin yawan al’umma da mabanbantan kabilu da ma mabiya addinai da Sin take da su da kuma zaman lafiya da ci gaban da suke morewa a kasar a matsayin abun koyi a duniya. Wadannan abubuwa da na zayyana, sun nuna karfi da gogewar Sin a harkokin da suka shafi tabbatar da zaman lafiya ba tare da zubar da jini ko tashin hankali ba. Haka kuma sun nuna cewa za ta iya taka rawa wajen tabbatar da kwanciyar hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Mun Damu Da Matsalar Yara 'Yan Shila A Adamawa - Fintiri

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.