• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Japan Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta Kan Zuba Dagwalon Ruwan Nukiliya Cikin Teku

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wajibi Ne Japan Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta Kan Zuba Dagwalon Ruwan Nukiliya Cikin Teku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da kasar Japan take dab da zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, Vincent Kelly, mazaunin wani tsibiri da ke tekun Pasifik ya kara bayyana damuwa, yana mai cewa, shirin Japan na zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, kuskure ne, wanda zai haifar da bala’i.

Ana fatan hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa wato IAEA da ke ziyara a Japan za ta yi bincike bisa sanin ya kamata, da adalci, a matsayin kwararriya, kan aikin Japan na zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, a kokarin kiyaye tsaron kasa da kasa.

  • Kasar Sin Ta Tuntuba Tare Da Musayar Ra’ayi Da Dukkan Bangarori Game Da Warware Rikicin Ukraine A Siyasance

Tun daga jiya 29 ga wata, kwararrun hukumar IAEA suka fara ziyararsu ta kwanaki 5 a Japan. Kafofin yada labaru na Japan sun ruwaito cewa, wannan ne karo na karshe da hukumar za ta yi bincike kan aikin zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, kafin ta gabatar da rahoton nazarinta na karshe.

Rafael Mariano Grossi, babban sakataren IAEA ya bayyana a fili yayin da ya ziyarci kasar Sin a kwanan baya cewa, hukumar ba ta amince ba, kuma ba ta goyon bayan shirin duk wata kasa na zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, kuma ba za ta yarda da ayyukan da suka saba wa mizanin tsaro na duniya ba.

Yayin da kasashen duniya ke kin yarda da kuma nuna shakku kan shirinta na zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, bai kamata gwamnatin Japan ta nemi samun iznin zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku daga wajen hukumar IAEA ba.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Yau shekaru 12 da suka gabata, hadarin nukiliya na Fukushima ya haifar da babban bala’i ga duniya. Yanzu Japan tana yunkurin illata moriyar bai daya ta daukacin bil’Adama, domin samun moriyarta ta gajeren lokaci. Dole ne a ki yarda da abin da Japan take yi.

Kamata ya yi Japan ta sauke nauyin dake wuyanta, ta tattauna da kasashe makwabtanta da hukumomin kasa da kasa masu ruwa da tsaki, domin cimma daidaito. Kafin haka kuma, kada Japan ta yi gaban kanta wajen zuba dagwalon ruwan nukiliya cikin teku. (Tasallah Yuan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Kama Aiki A Fadar Shugaban Kasa

Next Post

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Gana Da Kyari, Emefiele Kan Cire Tallafin Man Fetur

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

6 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

7 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

8 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

9 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

10 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

20 hours ago
Next Post
Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Gana Da Kyari, Emefiele Kan Cire Tallafin Man Fetur

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Gana Da Kyari, Emefiele Kan Cire Tallafin Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.