• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Girbe Ta

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Girbe Ta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Mun yi karya da yaudara da sata, mun kuma samar da darussa na musamman na koyar da ayyukan, wadanda suka kasance abubuwan da muke alfahari da su na tabbatar da ci gaban kasar Amurka.” Kalaman tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ke nan, don gane da irin abubuwan kunya da Amurka ta aikata ba tare da boyewa ba a shekarun baya. Lallai a kan batun yaudara, Mr.Pompeo ya fadi gaskiya.

 

A kwanan nan kuma, a karon farko cikin shekaru 12, rundunar sojin Amurka ta wallafa tsarin tafiyarwa mai lakabin “Yaudara”, wato wani salo da ake amfani da shi wajen yaudarar abokan gaba da kitsa karairayi, matakin da ya ba kasashen duniya mamaki matuka.

  • Zanga-zanga: Birtaniya, Amurka Da Kanada Sun Gargadi ‘Yan Kasarsu Mazauna Nijeriya
  • Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

A hakika, domin cimma burinta, har kullum Amurka ba ta jin kunyan aikata karya da yaudara da kuma sata, a maimakon haka, tana alfahari da su. Kuma ba a fannin soja kawai Amurka take yaudara ba, ma iya cewa hakan ya zame wa kasar jini da tsoka. Idan ba mu manta ba, a tsakiyar karni na 20, hukumar leken asiri ta CIA ta Amurka, ta fara aiwatar da shirin da aka san shi da suna “Operation Mockingbird”, shirin da ke yunkurin sayen ’yan jarida da wasu hukumomin kasa da kasa don samun bayanan sirri, kuma har zuwa yanzu, kana hukumar CIA ita ma tana kokarin sarrafa kafofin yada labarai ta hanyar sayen ma’aikatansu.

 

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Kaza lika a shekarar 2003, tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Colin Powell, ya zargi kasar Iraki da nazari kan makamai masu guba, tare da nuna farin garin da ya samu a gun taron kwamitin sulhun MDD, kuma da wannan dalili ne sojojin hadin kai na Amurka da Birtaniya, suka kaddamar da yaki a kan Irakin, amma har zuwa yanzu, Amurka ba ta iya nuna hakikanin shaida mallakar makaman kare dangi a Iraki ba.

 

Ban da haka, Amurka ta kaddamar da yaki a kan Syria, bisa dalilin wai sojojin gwamnatin kasar sun yi amfani da makamai masu guba, amma ga shi sojojin kasar Amurka da ke Syria na satar albarkatun mai da alkama na Syria a kowace rana, tare da yin jigilarsu zuwa ketare.

 

Domin dakile kasar Sin kuma, Amurka ta yayata karairayi na shafa wa kasar bakin fenti, a kan manufofinta game da jihar Xinjiang, har ma ta yada karairayi game da alluran rigakafi da kasar Sin ta samar a yayin da ake fama da annobar COVID-19, ba tare da yin la’akari da lafiyar al’ummar kasashe masu tasowa wadanda ke tsananin bukatar rigakafin ba.

 

Irin wadannan abubuwa ba za su lissafu ba, wadanda suka kasance shaida ta “karya da yaudara da sata” da ’yan siyasar Amurka suka bayyana. Don haka abun tambaya a nan shi ne wace ce ke yada karairaiyi a fadin duniya, kuma wace ce ke gudanar da ayyuka na gurgunta fahimtar al’umma a kan wasu kasashe, kana kuma wace ce ke ta kutsen yanar gizo? Kasashen duniya sun san amsar hakan, kuma Amurka ta ci amana ta hanyar aikata munanan abubuwa.

 

Kamata ya yi Amurka ta daina yada karairayi, ta daina yaudarar al’ummar kasashen duniya, kuma ta daina shafa wa sauran kasashe kashin kaji. Kamar yadda Bahaushe kan ce, wanda ya shuka zamba, shi zai girbe ta! (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Sarkin Gobir Da Wasu Mutane 5 A Sokoto

Next Post

Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr – Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

18 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

6 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

7 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr – Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr - Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.