• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Girbe Ta

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Girbe Ta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Mun yi karya da yaudara da sata, mun kuma samar da darussa na musamman na koyar da ayyukan, wadanda suka kasance abubuwan da muke alfahari da su na tabbatar da ci gaban kasar Amurka.” Kalaman tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ke nan, don gane da irin abubuwan kunya da Amurka ta aikata ba tare da boyewa ba a shekarun baya. Lallai a kan batun yaudara, Mr.Pompeo ya fadi gaskiya.

 

A kwanan nan kuma, a karon farko cikin shekaru 12, rundunar sojin Amurka ta wallafa tsarin tafiyarwa mai lakabin “Yaudara”, wato wani salo da ake amfani da shi wajen yaudarar abokan gaba da kitsa karairayi, matakin da ya ba kasashen duniya mamaki matuka.

  • Zanga-zanga: Birtaniya, Amurka Da Kanada Sun Gargadi ‘Yan Kasarsu Mazauna Nijeriya
  • Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

A hakika, domin cimma burinta, har kullum Amurka ba ta jin kunyan aikata karya da yaudara da kuma sata, a maimakon haka, tana alfahari da su. Kuma ba a fannin soja kawai Amurka take yaudara ba, ma iya cewa hakan ya zame wa kasar jini da tsoka. Idan ba mu manta ba, a tsakiyar karni na 20, hukumar leken asiri ta CIA ta Amurka, ta fara aiwatar da shirin da aka san shi da suna “Operation Mockingbird”, shirin da ke yunkurin sayen ’yan jarida da wasu hukumomin kasa da kasa don samun bayanan sirri, kuma har zuwa yanzu, kana hukumar CIA ita ma tana kokarin sarrafa kafofin yada labarai ta hanyar sayen ma’aikatansu.

 

Labarai Masu Nasaba

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Kaza lika a shekarar 2003, tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Colin Powell, ya zargi kasar Iraki da nazari kan makamai masu guba, tare da nuna farin garin da ya samu a gun taron kwamitin sulhun MDD, kuma da wannan dalili ne sojojin hadin kai na Amurka da Birtaniya, suka kaddamar da yaki a kan Irakin, amma har zuwa yanzu, Amurka ba ta iya nuna hakikanin shaida mallakar makaman kare dangi a Iraki ba.

 

Ban da haka, Amurka ta kaddamar da yaki a kan Syria, bisa dalilin wai sojojin gwamnatin kasar sun yi amfani da makamai masu guba, amma ga shi sojojin kasar Amurka da ke Syria na satar albarkatun mai da alkama na Syria a kowace rana, tare da yin jigilarsu zuwa ketare.

 

Domin dakile kasar Sin kuma, Amurka ta yayata karairayi na shafa wa kasar bakin fenti, a kan manufofinta game da jihar Xinjiang, har ma ta yada karairayi game da alluran rigakafi da kasar Sin ta samar a yayin da ake fama da annobar COVID-19, ba tare da yin la’akari da lafiyar al’ummar kasashe masu tasowa wadanda ke tsananin bukatar rigakafin ba.

 

Irin wadannan abubuwa ba za su lissafu ba, wadanda suka kasance shaida ta “karya da yaudara da sata” da ’yan siyasar Amurka suka bayyana. Don haka abun tambaya a nan shi ne wace ce ke yada karairaiyi a fadin duniya, kuma wace ce ke gudanar da ayyuka na gurgunta fahimtar al’umma a kan wasu kasashe, kana kuma wace ce ke ta kutsen yanar gizo? Kasashen duniya sun san amsar hakan, kuma Amurka ta ci amana ta hanyar aikata munanan abubuwa.

 

Kamata ya yi Amurka ta daina yada karairayi, ta daina yaudarar al’ummar kasashen duniya, kuma ta daina shafa wa sauran kasashe kashin kaji. Kamar yadda Bahaushe kan ce, wanda ya shuka zamba, shi zai girbe ta! (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Garkuwa Da Sarkin Gobir Da Wasu Mutane 5 A Sokoto

Next Post

Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr – Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

Related

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

17 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

4 days ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

1 week ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

1 week ago
Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

2 weeks ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

2 weeks ago
Next Post
Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr – Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr - Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.