• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Girbe Ta

bySulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Zamba

“Mun yi karya da yaudara da sata, mun kuma samar da darussa na musamman na koyar da ayyukan, wadanda suka kasance abubuwan da muke alfahari da su na tabbatar da ci gaban kasar Amurka.” Kalaman tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ke nan, don gane da irin abubuwan kunya da Amurka ta aikata ba tare da boyewa ba a shekarun baya. Lallai a kan batun yaudara, Mr.Pompeo ya fadi gaskiya.

 

A kwanan nan kuma, a karon farko cikin shekaru 12, rundunar sojin Amurka ta wallafa tsarin tafiyarwa mai lakabin “Yaudara”, wato wani salo da ake amfani da shi wajen yaudarar abokan gaba da kitsa karairayi, matakin da ya ba kasashen duniya mamaki matuka.

  • Zanga-zanga: Birtaniya, Amurka Da Kanada Sun Gargadi ‘Yan Kasarsu Mazauna Nijeriya
  • Me Ya Sa Manyan Shugabannin Kamfanonin Amurka Ke Ziyaratar Sin A Wannan Lokaci?

A hakika, domin cimma burinta, har kullum Amurka ba ta jin kunyan aikata karya da yaudara da kuma sata, a maimakon haka, tana alfahari da su. Kuma ba a fannin soja kawai Amurka take yaudara ba, ma iya cewa hakan ya zame wa kasar jini da tsoka. Idan ba mu manta ba, a tsakiyar karni na 20, hukumar leken asiri ta CIA ta Amurka, ta fara aiwatar da shirin da aka san shi da suna “Operation Mockingbird”, shirin da ke yunkurin sayen ’yan jarida da wasu hukumomin kasa da kasa don samun bayanan sirri, kuma har zuwa yanzu, kana hukumar CIA ita ma tana kokarin sarrafa kafofin yada labarai ta hanyar sayen ma’aikatansu.

 

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Kaza lika a shekarar 2003, tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Colin Powell, ya zargi kasar Iraki da nazari kan makamai masu guba, tare da nuna farin garin da ya samu a gun taron kwamitin sulhun MDD, kuma da wannan dalili ne sojojin hadin kai na Amurka da Birtaniya, suka kaddamar da yaki a kan Irakin, amma har zuwa yanzu, Amurka ba ta iya nuna hakikanin shaida mallakar makaman kare dangi a Iraki ba.

 

Ban da haka, Amurka ta kaddamar da yaki a kan Syria, bisa dalilin wai sojojin gwamnatin kasar sun yi amfani da makamai masu guba, amma ga shi sojojin kasar Amurka da ke Syria na satar albarkatun mai da alkama na Syria a kowace rana, tare da yin jigilarsu zuwa ketare.

 

Domin dakile kasar Sin kuma, Amurka ta yayata karairayi na shafa wa kasar bakin fenti, a kan manufofinta game da jihar Xinjiang, har ma ta yada karairayi game da alluran rigakafi da kasar Sin ta samar a yayin da ake fama da annobar COVID-19, ba tare da yin la’akari da lafiyar al’ummar kasashe masu tasowa wadanda ke tsananin bukatar rigakafin ba.

 

Irin wadannan abubuwa ba za su lissafu ba, wadanda suka kasance shaida ta “karya da yaudara da sata” da ’yan siyasar Amurka suka bayyana. Don haka abun tambaya a nan shi ne wace ce ke yada karairaiyi a fadin duniya, kuma wace ce ke gudanar da ayyuka na gurgunta fahimtar al’umma a kan wasu kasashe, kana kuma wace ce ke ta kutsen yanar gizo? Kasashen duniya sun san amsar hakan, kuma Amurka ta ci amana ta hanyar aikata munanan abubuwa.

 

Kamata ya yi Amurka ta daina yada karairayi, ta daina yaudarar al’ummar kasashen duniya, kuma ta daina shafa wa sauran kasashe kashin kaji. Kamar yadda Bahaushe kan ce, wanda ya shuka zamba, shi zai girbe ta! (Mai Zane:Mustapha Bulama)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr – Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

Sabon Mafi Ƙarancin Albashi Zai Laƙume ₦6.2tr - Godswill Akpabio Daga cikin Kasafin Bana

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version