• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya na tashar Fukushima cikin teku, kasar ta fuskanci matsala wajen sayar da abincin ruwanta. Bisa labaran da kafofin yada labarai na kasar suka bayar, an ce, a ma’adanai na wasu kamfanonin sarrafa abincin ruwa na kasar, tarin abincin ruwa na Scallop da dai sauransu sun kusan kai rufin ma’adanan da ke da tsayin mita 8. 

An ce, a shekarar bara, gaba dayan kudin abincin ruwa da Japan ta sayar ga kasashen duniya ya kai dala biliyan 1.97. Amma tun bayan da Japan din ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku, yawan abincin ruwan da kasar ke sayarwa ga waje ya ragu da matukar yawa, har ma wasu masanan sun yi hasashen raguwar za ta iya kai kaso 50%. Ban da wannan, sakamakon yadda sassan kasa da kasa ke nuna kyamar matakin na Japan, harkokin yawon shakatawa na kasar ma na fuskantar munanan asarori.

  • Sakamako Da Aka Samu Bayan Gina Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya
  • Jamaica Na Neman Greenwood Ya Koma Wakiltarta A Kwallon Kasa

Sinawa kan ce “an tsinci ridi, a yayin da kuma aka yi watsi da kankana”, wajen bayyana yadda akan sha babbar hasara sakamakon neman cin karamar riba, to, abin da Japan ke yi ke nan yanzu, sakamakon yadda ta zubar da dagwalon nukiliyarta cikin teku don neman yin tsimin kudi, amma a sa’i daya, tana kashe makudan kudade wajen wanke kanta daga zarge-zarge da ake mata, tare kuma da shan munanan hasarori ta fannonin tattalin arziki. Lallai ma iya cewa, wanda ya shuka zamba, shi zai yi girbinta.

Tun daga ranar 5 ga wata, a zagaye na biyu ne Japan ta sake fara zubar da ruwan dagwalon nukiliyarta cikin teku, aikin da za ta shafe kimanin kwanaki 17 tana yi a wannan zagaye. Gaba dayan ruwan dagwalon nukiliya da ake ajiye da shi a tashar Fukushima ya kai sama da ton miliyan 1.3, kuma an yi hasashen za a shafe a kalla shekaru 30 kafin an zubar da gaba dayansa cikin teku. Don haka, da wuya mu iya hasashen yadda tekunan duniyarmu za su kasance, kuma ko halittun teku za su ci gaba da rayuwa ko a’a, da kuma yaya duniyarmu za ta kasance, da ma wace masifa matakin zai janyo wa dan Adam.

Muna yi wa gwamnatin Japan gargadi da ta dakatar da wannan mugun aikin nan da nan, kuma ta dauki matakan da suka dace, don kiyaye teku na dukkanin ’yan Adam. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Yabon Dan Kuturu…

Next Post

Charles Onunaiju: Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Sanya Sabon Ci Gaba A Nijeriya

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

18 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

19 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

20 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

21 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

22 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

23 hours ago
Next Post
Charles Onunaiju: Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Sanya Sabon Ci Gaba A Nijeriya

Charles Onunaiju: Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Sanya Sabon Ci Gaba A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.