• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi: Amurka Ba Ta Da Alfarma Ko Gatan Kin Biyayya Ga Dokokin Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi: Amurka Ba Ta Da Alfarma Ko Gatan Kin Biyayya Ga Dokokin Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiya Alhamis, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da ’yan jaridu tare da takwararsa ta kasar Indonesia Retno Marsudi a birnin Jakarta, fadar mulkin kasar Indonesia. 

A yayin taron, an ce a halin yanzu, gamayyar kasa da kasa na yin kira da a gaggauta tsagaita bude wuta a yankin Gaza, yayin da ake kira ga kwamitin sulhu na MDD da ya ba da gudummawarsa kan wannan aiki. Game da tambayar ko mene ne matsayin kasar Sin kan wannan batu? Wang Yi ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu, rikicin yankin Gaza ya tsawaita zuwa rabin shekara, wanda ya haddasa mummunar barazanar jin kai da ba a taba ganin irin ta ba cikin karni na 21.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Neman Zama Madaukakiya Tare Da Sake Waiwayar Dokokin Kasa Da Kasa
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwararsa Ta Afirka Ta Tsakiya

Ya ce kwamitin sulhun MDD ya amsa kiran gamayyar kasa da kasa, kuma yana ci gaba da binciken daftarin tsagaita bude wuta a yankin Gaza, amma, sau da yawa, kasar Amurka ita kanta kadai ta yi ta watsi da daftarori masu nasaba da hakan.

Kwanan baya, a karo na farko, kwamitin sulhun MDD ya zartas da kuduri mai lamba 2728, inda aka yi kira da a tsagaita bude wuta a yankin Gaza, amma kasar Amurka ta ce daftarin ba shi da ikon hana ko wane bangare daukar mataki. Lamarin da ya bata ran kasashen duniya, ya kuma bayyana yadda kasar Amurka take son yi wa kasashen duniya mulkin kashin kai. Kaza lika hakan na nuna cewa, kasar Amurka tana bin manufar idan tana so, za ta bi dokokin kasa da kasa, amma idan ba ta so, shi ke nan, za ta yi kyamar dokokin.

Wang Yi ya kara da cewa, kasar Amurka, ba ta da alfarma ko gatan kin biyayya ga dokokin kasa da kasa. Don haka ake fatan Amurkan za ta daidaita tsohon ra’ayinta, tare da nuna goyon baya ga kuduri mai lamba 2728 a matsayin mambar MDD, domin yin hadin gwiwa da sauran kasashen duniya wajen cimma burin tsagaita bude wuta a yankin Gaza.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

(Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

Related

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

2 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

2 hours ago
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

14 hours ago
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

15 hours ago
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

16 hours ago
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

17 hours ago
Next Post
Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.