ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Chibok

Shekara 10 kenan da sace ‘yan mata 276 na makarantar sakandaren gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno, an fitar da wani sabon rahoto da ke nuna cewa ‘yan mata 21 daga cikin wadanda aka sako ya zuwa yanzu sun dawo gida tare da yara 34.

Wannan yana cikin rahoton da Gidauniyar Murtala Muhammed (MMF) ta fitar ta kuma ta raba wa manema labarai a karshen mako a Abuja.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Shari’ar Zargin Karkatar Da Dukiyar Al’umma: Ganduje Da Iyalansa Ba Su Halarci Kotu Ba

Kamar yadda gidauniyar ta ce, rahoton an yi shi ne domin tunawa da cika shakara 10 da sace ‘yan matan. Rahoton ya kuma tabbatar da cin zarafi da auren dole da ‘yan matan suka fuskanta a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan ta’addan.

ADVERTISEMENT

Haka kuma rahoton na gidauniyar ya kara bayyana cewa iyayen daliban aka sace su 48 ne suka mutu. Sauran iyayen daliban da ke raye kuma na rayuwa cikin tashin hankali da fargabar rashin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Babban Daraktan gidauniyar MMF, Dakta Aisha Muhammad-Oyebode wacce ta gabatar da rahoton ta bayyana cewa, gidauniyar ta lissafa wasu muhimman shawarwari guda 10.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Gidauniyar ta ce ya kamata gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da kasashen duniya su ba da fifiko a kan wadannan shawarwari. Shawarwarin sun hada da, daukar ingantattun matakan tsaro, shirye-shiryen tallafa wa kuyuka da tsarin ankararwa cikin gaggawa dangane da barazanar tsaro.

Ta ce, “A cikin shekara 10 tun lokacin da aka yi garkuwa da ‘yan matan Chibok ya janyo fusata al’ummar duniya gaba daya, kowani al’amari ya sauya a Nijeriya, inda masu garkuwa da mutane ke ci gaba da cin karansu babu babbaka na tsawon shekaru masu yawa.

“A daidai lokacin da Nijeriya ke fama da annoban garkuwa da mutane wanda ba ta nuna alaman raguwa ba, muna kira ga hukumomin Nijeriya da na kasa da kasa su dauki muhimman matakai domin magance abubuwan da ke janyo rikice-rikice da tashin hankali kan mata, wadanda suka hada da fatara, rashin natsuwa da tabarbarewar tattalin arziki.

“Rahoton ya gano cewa cikin 91 na daliban makarantar guda 276 har yanzu ba su san inda aka dosa ba.

“Rahoton ya kuma bayyana cewa ‘yan matan Chibok 21 da aka sako sun samu sun dawo da yara 34, wanda ya nuna sun fuskanci cin zarafi na jin jima’I da su da kuma tilasta musu yin auren dole lokacin da suke tsare.

“Rahoton MMF ya bayar da shawarar cewa a yi kokarin magance tushen yin garkuwa da mutane, sannan ya bukaci karfafa hadin gwiwa na kasa da kasa wajen daukar matakan kawo karshen lamarin.”

Ta kuma bayar da shawarar a dauki matakin tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu kan wannan mummunan labari komin matsayin da suke da shi doka ta yi aiki a kan kowa.

Chibok
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.