• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Gana Da Bakin Kasashen Larabawa Da Suka Halarci Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Hadin-kan Kasar Sin Da Kasashen Larabawa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Ya Gana Da Bakin Kasashen Larabawa Da Suka Halarci Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Hadin-kan Kasar Sin Da Kasashen Larabawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jiya Jumma’a 31 ga watan Mayu, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da wasu baki daga kasashen Larabawa, da suka zo kasar Sin don halartar taron ministoci karo na 10, na dandalin tattauna hadin-kan kasar Sin da kasashen Larabawa.

A yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Somaliya, Ahmed Moallim Fiqi, minista Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan kasar Somaliya sosai, wajen kiyaye mulkin kai da cikakken yankin ta, kana tana mara mata baya kan kokarin da take yi na tabbatar da zaman karko a fannin siyasa, da inganta samar da tsaro, da kuma aiwatar da manufofin sake raya tattalin arziki. Wang Yi ya kara da cewa, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, a wasu muhimman fannoni, ciki har da aikin gona, da kamun kifi, da kiwon lafiya da dai sauransu, da kuma sa kaimi ga aiwatar da jerin shawarwarin kasa da kasa da kasar Sin ta gabatar, kamar raya shawarar “Ziri daya da hanya daya” a kasar Somaliya.

  • Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar
  • Hakkin Bil Adam Iri Na Amurka Matakin Gatanci Da Babakere Ne

A nasa bangaren, minista Fiqi ya bayyana cewa, kasar Sin ta zama ma’auni, kuma fitila ga kasashe masu tasowa. Somaliya na fatan kara yin hadin gwiwa tare da Sin a fannonin samar da ababen more rayuwa, da makamashi, da zuba jari, da kiwon lafiya, da tsaro, da dai sauransu, a karkashin tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, da na Sin da kasashen Larabawa.

A yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Comoros, Dhoihir Dhoulkamal, minista Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwa tare da Comoros, a fannoni daban daban, wadanda suka shafi kawar da fatara, da ba da ilimi da horo, da kiwon lafiya da sauransu, da kuma kara shigo da kayayyaki masu inganci daga kasar Comoros.

A nasa bangaren, minista Dhoulkamal ya ce, kasarsa ta amince sosai da muhimmiyar shawarar da shugaba Xi Jinping ya gabatar, kan hadin gwiwar Sin da kasashen Larabawa. Kaza lika, ta nuna tsayayyen goyon baya ga bangaren Sin, wajen kiyaye cikakken yankin kasa. A cewar ministan, shawarar “Ziri daya da hanya daya”, tana taimaka wa kasashen Larabawa da na Afirka, wajen samun ci gaba tare, kuma kasar Comoros za ta ci gaba da himmatuwa wajen shiga cikinta. (Bilkisu Xin)

Labarai Masu Nasaba

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amfani Da Makami Mai Linzami A Ukraine: Putin Ya Gargadi Kasashen Yammacin Duniya

Next Post

Sirrin Zaman Lafiyar Da Ake Mora A Jihar Nasarawa –Kakakin Gwamnan Jihar

Related

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

10 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

11 hours ago
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

12 hours ago
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

13 hours ago
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

14 hours ago
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

15 hours ago
Next Post
Wang yi

Sirrin Zaman Lafiyar Da Ake Mora A Jihar Nasarawa –Kakakin Gwamnan Jihar

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.