ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Gana Da Bakin Kasashen Larabawa Da Suka Halarci Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Hadin-kan Kasar Sin Da Kasashen Larabawa

by CGTN Hausa
2 years ago
Wang yi

Jiya Jumma’a 31 ga watan Mayu, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya gana da wasu baki daga kasashen Larabawa, da suka zo kasar Sin don halartar taron ministoci karo na 10, na dandalin tattauna hadin-kan kasar Sin da kasashen Larabawa.

A yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Somaliya, Ahmed Moallim Fiqi, minista Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan kasar Somaliya sosai, wajen kiyaye mulkin kai da cikakken yankin ta, kana tana mara mata baya kan kokarin da take yi na tabbatar da zaman karko a fannin siyasa, da inganta samar da tsaro, da kuma aiwatar da manufofin sake raya tattalin arziki. Wang Yi ya kara da cewa, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, a wasu muhimman fannoni, ciki har da aikin gona, da kamun kifi, da kiwon lafiya da dai sauransu, da kuma sa kaimi ga aiwatar da jerin shawarwarin kasa da kasa da kasar Sin ta gabatar, kamar raya shawarar “Ziri daya da hanya daya” a kasar Somaliya.

  • Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar
  • Hakkin Bil Adam Iri Na Amurka Matakin Gatanci Da Babakere Ne

A nasa bangaren, minista Fiqi ya bayyana cewa, kasar Sin ta zama ma’auni, kuma fitila ga kasashe masu tasowa. Somaliya na fatan kara yin hadin gwiwa tare da Sin a fannonin samar da ababen more rayuwa, da makamashi, da zuba jari, da kiwon lafiya, da tsaro, da dai sauransu, a karkashin tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, da na Sin da kasashen Larabawa.

ADVERTISEMENT

A yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Comoros, Dhoihir Dhoulkamal, minista Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwa tare da Comoros, a fannoni daban daban, wadanda suka shafi kawar da fatara, da ba da ilimi da horo, da kiwon lafiya da sauransu, da kuma kara shigo da kayayyaki masu inganci daga kasar Comoros.

A nasa bangaren, minista Dhoulkamal ya ce, kasarsa ta amince sosai da muhimmiyar shawarar da shugaba Xi Jinping ya gabatar, kan hadin gwiwar Sin da kasashen Larabawa. Kaza lika, ta nuna tsayayyen goyon baya ga bangaren Sin, wajen kiyaye cikakken yankin kasa. A cewar ministan, shawarar “Ziri daya da hanya daya”, tana taimaka wa kasashen Larabawa da na Afirka, wajen samun ci gaba tare, kuma kasar Comoros za ta ci gaba da himmatuwa wajen shiga cikinta. (Bilkisu Xin)

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Wang yi

Sirrin Zaman Lafiyar Da Ake Mora A Jihar Nasarawa –Kakakin Gwamnan Jihar

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.