• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bayani Game Da Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

by Sulaiman and CMG Hausa
3 years ago
Wang Yi

Jiya Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Amurka Joe Biden, a tsibitin Bali na kasar Indonesiya. Bayan ganawar ta su, mamban majalisar gudanarwa, kana ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi karin bayani ga kafofin watsa labarai game da ganawar shugabannin biyu.

Wang Yi ya ce, ganawar shugabannin biyu na da muhimmiyar maana, domin wannan shi ne karo na farko da shugaban kasar Sin da na Amurka suka yi ganawa fuska ta fuska cikin shekaru 3 da suka gabata, kuma karo na farko da shugabannin biyu suka gana da juna fuska ta fuska, bayan shugaban kasar Amurka Joe Biden ya kama aiki. Kaza lika, wannan shi ne karo na farko, da shugabannin koli na kasar Sin da na Amurka suka yi muamala, bayan sun kammala muhimman taruka cikin kasashensu.

Game da batun dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, Wang Yi ya ce, a yayin ganawar shugabannin biyu, an tabbatar da cewa, za a magance tabarbarewar dangantaka a tsakanin kasashen biyu, yayin da ake neman wata hanyar da ta dace ta daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka. Kuma, za a tattauna cikin hadin gwiwa, domin fidda manufar daidaita dangantaka tsakanin kasashen biyu.

Saan nan kuma, an fara yunkurin aiwatar da raayin shugabannin biyu, ta yadda za a daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu cikin yanayin zaman karko.
Haka kuma, a yayin ganawar tasu, shugabannin biyu sun mai da hankali kan batun lardin Taiwan na kasar Sin. Wang Yi ya ce, kasar Sin na fatan Amurka za ta aiwatar da matakai masu nasaba da hakan, kamar yadda ta bayyana, da kuma bin manufar kasar Sin kasa daya tak a duniya”, da sanarwar hadin gwiwa guda uku da kasar Sin da Amurka suka kulla, da kaucewa bata yanayin lardin Taiwan.

Dangane da wannan batu, shugaba Biden ya ce, kasar Amurka tana tsayawa tsayin daka kan manufar kasar Sin kasa daya tak a duniya, kuma ba ta goyon bayan ballewar yankin Taiwan daga kasar Sin, kana kasar Amurka ba ta da burin hana bunkasuwar kasar Sin ta hanyar rura wutar batun Taiwan.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Dangane da ci gaban da kasashen biyu suka samu a fannin habaka hadin gwiwa bisa fannoni daban daban, Wang Yi ya ce, a yayin ganawar shugabannin biyu, shugaba Xi Jinping ya ce, bai kamata a dakatar da aikin raya dangantaka a tsakanin kasar Sin da kasar Amurka sakamakon bambancinsu ba, kuma ya kamata kasashen biyu su dukufa wajen tsawaita jerin hadin gwiwar dake tsakaninsu.

Bugu da kari, a yayin ganawar tasu, shugaba Xi ya bayyana matsayin kasar Sin kan wasu batutuwan dake janyo hankulan kasar Amurka, da ma sauran kasashen duniya.

Shugabannin biyu, sun kuma yi musayar raayoyi kan batutuwan dake shafar kasar Ukraine, da batun nukiliyar zirin Koriya da dai sauransu. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
Ganduje Ya Karrama Dan Sandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Dala $200,000 A Kano

Ganduje Ya Karrama Dan Sandan Da Ya Ki Karbar Cin Hancin Dala $200,000 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.