• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Cikakken Bayani Kan Matsayar Sin Game Da Yankin Taiwan

by CMG Hausa
3 years ago
Wang Yi

Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya kira taron ganawa da manema labarai a yammacin jiya, bayan ya halarci tarukan ministocin harkokin wajen kasashen gabashin Asiya da aka shirya a birnin Phnom Penh, fadar mulkin kasar Cambodia domin kyautata hadin gwiwa a tsakaninsu. 

Yayin taron manema labaran, Wang Yi ya ce, “Shugabar majalisar wakilan Amurka Nancy Pelosy, ta yi watsi da adawar gwamnatin kasar Sin, ta kai ziyara yankin Taiwan, bisa amincewar gwamnatin kasar Amurka”.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

Ya ce a bayyane yake cewa, ziyararta ta keta ‘yancin mulkin kan kasar Sin, kuma ta tsoma baki cikin harkokin gidan kasar, haka kuma ta sabawa alkawarin gwamnatin Amurka, tare kuma da lahanta zaman lafiya da kwanciyar hankali a zirin Taiwan.

Don haka, tabbas kasar Sin ta mayar da martani ta hanyar daukan matakai masu karfi da suka dace bisa matsayar adalci.

Kuma ko shakka babu, atisayen soja da rundunar sojojin kasar Sin take yi a fili, ya dace da dokar kasar, da ta kasa da kasa, da kuma ka’idojin kasa da kasa.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

A cewar Wang Yi, manufar ita ce, yi wa masu tayar da tarzoma kashedi, da kuma hukunta masu neman ‘yancin kan Taiwan.

Haka kuma, za a ci gaba da daukar matakan da suka dace domin kiyaye ‘yancin mulkin kan kasar Sin da yankunan kasar, da murkushe yunkurin Amurka na hana ci gaban kasar Sin bisa fakewa da batun yankin Taiwan, tare kuma da murkushe makarkashiyar mahukuntan yankin Taiwan na neman ‘yancin kai bisa dogaro da goyon bayan Amurka.

Bugu da kari, Wang Yi ya ce kasar Sin na kokarin kare dokar kasa da kasa, da ka’idar huldar dake tsakanin kasa da kasa, musamman ma ka’idar rashin tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe ta MDD, yana mai cewa, “Idan aka yi watsi da ka’idar, manyan kasashe kamar Amurka za su zalunci kananan kasashe kamar yadda suke so, amma ba zai yiyu kasar Sin ta amince da faruwar irin wannan al’amari ba, kuma ya dace kasashen duniya su hada kai domin hana koma bayan wayewar kan bil Adam.” (Mai fassarawa: Jamila daga CMG Hausa)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Next Post
Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU – Malamar Jami’ar Oyo

Na Koma Sayar Da Dankalin Turawa Ne Sakamakon Yajin Aikin ASUU - Malamar Jami'ar Oyo

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.