• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich

byCGTN Hausa
2 years ago
Wang yi

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi tir da karairayin da ake yadawa game da kisan kiyashi da kuma tilastawa mutane yin aiki a jihar Xinjiang, sannan ya yi kira da a yi kokarin kauce wa ra’ayin “tabka hasara” a yayin da yake amsa tambayoyi a taron tsaro na Munich a ranar Asabar.

Wang Yi ya ce, tun lokacin da aka kafa yankin Xinjiang na kabilar Uygur mai cin gashin kansa, yawan mutanen Uygur ya karu daga miliyan 3 zuwa sama da miliyan 12 ya zuwa yanzu. Kuma ana ba da kariya ga ‘yancin gudanar da addini na dukkan kabilu da ke wurin, inda ya ba da misali da cewa musulmai na da isasshen wuraren ibada kuma gwamnati ta dauki nauyin gyara da kula da masallatai.

  • Wang Yi: Sin Ta Sha Alwashin Zama Jigon Samar Da Daidaito A Duniya Mai Tangal-Tangal
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Kara Amfani Da Filaye Don Bunkasuwar Yankuna Mai Inganci

Da yake magana game da zargin da ake yi cewa ana tilastawa mutane yin aiki, Wang ya ce, yin amfani da wannan zargi a matsayin uzuri don shafawa kasar Sin bakin fenti, wata manufa ce ta kwace wa al’ummar Uygur ayyukan yi tare da hana su sayar da hajojinsu.

Ya kara da cewa, ci gaban da kasar Sin ta samu cikin sauri ya haifar da rashin jin dadi da damuwa a tsakanin mahukuntan wasu kasashe, shi ya sa suke yada karairayi game da jihar Xinjiang don haifar da cikas, ta yadda za a hana ci gaban kasar Sin da farfado da tattalin arzikinta.

Bugu da kari, Wang Yi ya ce, ra’ayin da wasu ke da shi na “tabka hasara”, ba zabi ne da hankali zai dauka ba, kuma cin nasara tare shi ne makomar dan Adam.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Rahoton na shekara-shekara da aka fitar a Litinin din nan gabanin kammala taron tsaro na Munich, ya jaddada damuwar da ake da ita kan ra’ayin “tabka hasara”, yayin da ake samun karuwar tashe-tashen hankula a fannin siyasa da karuwar rashin tabbas na tattalin arziki.

A cewar rahoton, gwamnatoci da dama ba sa mai da hankali kan cikakkiyar fa’idar hadin gwiwar duniya, maimakon haka suna kara nuna damuwa cewa, suna samun moriya kasa da ta saura.

Wang ya ce, rahoton ya nuna yadda nahiyar Turai ke tunani da kuma damuwar da duniya ke ciki.

Ya bayyana cewa, bangaren kasar Sin ya yi imanin cewa, ra’ayin cin moriya da faduwar wani, da neman bayar da wasu saniyar ware, da yunkurin yin fito-na-fito na wani gungu ne ke haifar da ra’ayin “tabka hasara”. Yana mai cewa, kasashe da yawa sun fahimci cewa, tilas ne a kaucewa hasara.

Ya kara da cewa, ya kamata mu yi aiki tare, mu yi la’akari da muradun wasu tare da kare muradun kanmu, da inganta ci gaban hadin gwiwa tare da neman ci gaban kanmu, ta yadda za mu samu nasara tare, kuma nasara shi ne burin da ya kamata mu bi tare.

Wang ya ce, idan har ana son cimma nasara tare, kamata ya yi kasashe su zabi hadin kai kan rarrabuwar kawuna, hadin gwiwa kan sabani da bude kofa ga juna.

A ranar 18 ga watan Fabrairu ne aka kammala taron kwanaki uku na taron tsaro na Munich karo na 60 a birnin Munich na kasar Jamus. A yayin taron, mahalarta daga kasashe daban-daban sun tattauna batutuwa kamar rikicin Ukraine, rikicin Isra’ila da Falasdinu da kuma tsarin kasa da kasa. (Masu Fassarawa: Muhammed Yahaya, Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Murja

Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version