• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Zai Halarci Taron Tsaro Na Munich Tare Da Ziyarar Aiki A Sifaniya Da Faransa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi Zai Halarci Taron Tsaro Na Munich Tare Da Ziyarar Aiki A Sifaniya Da Faransa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zai halarci taron karawa juna sani game da tsaro na Munich karo na 60, kana zai gudanar da ziyarar aiki a kasashen Sifaniya da Faransa.

Da take tabbatar da hakan cikin wata sanarwa a Alhamis din nan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning, ta ce yayin taron na Munich, Wang Yi zai gabatar da jawabi game da kasar Sin, da matsayarta don gane da muhimman batutuwan da suka shafi duniya bisa taken taron. Daga nan kuma zai ziyarci kasashen Sifaniya da Faransa, kana zai halarci taron tattaunawa tsakanin Sin da Faransa bisa manyan tsare-tsare a birnin Faris, tsakanin ranaikun 16 zuwa 21 ga watan nan na Fabrairu.

  • Gwamna Lawal Ya Karɓo Sakamakon Jarabawar WAEC Da Hukumar Ta Riƙe
  • Sin Ta Yi Kira Ga Kasashe Masu Ci Gaba Da Su Kara Samar Da Gudummawar Jin Kai Ga Kasashe Masu Tasowa Mabukata

Kaza lika cikin wata sanarwar ta daban, Mao Ning ta ce, a gabar da duniya ke fuskantar sauye-sauye a wannan karni, da sabon lokaci na canji da gargada, Wang zai fayyacewa taron na Munich matsayar Sin game da gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil Adama, kana zai yayata manufar samar da daidaito, da oda a tsarin duniya mai tasirin sassa daban daban.

A daya bangaren kuma, ziyarar da Wang zai kai Sifaniya, na zuwa ne yayin da alakar Sin da Sifaniya ke shiga shekaru 50 na biyu, kuma a wannan gaba Sin na fatan ziyarar za ta baiwa sassan 2 damar kara zurfafa aiwatar da ra’ayi daya na fahimtar juna da shugabanninsu suka cimma, da karfafa amincewa da juna, da yaukaka abota, da ingiza hadin gwiwa, da inganta cikakkiyar alakar sassan biyu daga dukkanin fannoni.

Bugu da kari, Wang zai zanta da tsagin kasar Faransa, zai kuma yi jagorancin taron tattaunawa na zabon zagaye tsakanin bangaren Sin da Faransa bisa manyan tsare-tsare.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Mao Ning ta kara da cewa, Sin na fatan yin aiki tare da Faransa, wajen kara zurfafa muhimmiyar tattaunawa, da yaukaka amincewa da juna ta fuskar siyasa, da ingiza hadin gwiwa a zahiri, da musaya tsakanin al’ummunsu, da musaya ta fannin al’adu. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NATOSinSiyasar Yemen
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jakadan Sin Ya Jaddada Aniyar Kasarsa Game Da Ba Da Gudummawar Shawo Kan Rikicin Siyasar Yemen

Next Post

Roy Hodgson Na Iya Rasa Aikinsa A Crystal Palace Idan Al’amura Suka Ci gaba A Haka

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

18 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

19 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

20 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

21 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

22 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

23 hours ago
Next Post
Roy Hodgson Na Iya Rasa Aikinsa A Crystal Palace Idan Al’amura Suka Ci gaba A Haka

Roy Hodgson Na Iya Rasa Aikinsa A Crystal Palace Idan Al'amura Suka Ci gaba A Haka

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.