ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Karɓo Sakamakon Jarabawar WAEC Da Hukumar Ta Riƙe

by Sulaiman
2 years ago
Gwamna Lawal

A ƙoƙarin da ya ke yi don ganin ya cika alƙawuran da ya yi wa Zamfarawa, musamman a harkar ilimi, Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samu nasarar karɓo sakamakon jarabawar WAEC na ‘yan asalin jihar, wanda Hukumar ta ƙi saki saboda rashin biyan kuɗin jarabawar.

Ita dai Hukumar da ke kula da shirya jarabawar ta WAEC ta riƙe sakamakon jarabawar ɗaliban jihar Zamfarar ne sakamakon bashin Naira Biliyan 1.4 da ta ke bin gwamnatocin jihar da suka gabata.

  • Zannan Bungudu Ya Gina Masallatai 20 Makarantun Islamiyya 15 A Jihar Zamfara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin ‘Pulaku’ Don Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawu Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa Gwamnan ya samu ganawa da shugabannin Hukumar ne a ofishin sa da ke Abuja ranar Litinin da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Ya ce, a ziyarar da suka kawo wa Gwamnan, sun samu ganawa da shugabannin Hukumar bisa jagorancin shugabar sashen mulki da harkokin kuɗi, Hajiya Binta Abdulkadir da kuma shugaban ofishin WAEC, Dr. Amos J. Dangut.

Ya ci gaba cewa, “A ƙoƙarin da gwamnatin nan ke yi na ganin ta haƙƙaƙa shirin ta na sanya dokar ta-ɓaci a harkar ilimi, Gwamna Dauda Lawal ya karɓi baƙuncin Shugabannin Hukumar WAEC a ofishin sa da ke Abuja.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Gwamnan, wanda ke tare da Kwamishinan ilimi, kimiyya da fasaha, Mallam Wadatau Madawaki, sun tattauna da shugabbanin Hukumar ta WAEC a kan abin da ya shafi basussukan da ake bin jihar Zamfara na gwamnatocin da suka gabata.

“Rashin biyan waɗannan kuɗaɗe na tsawon shekaru ya sa hukumar ta ƙi bayyana sakamakon jarabawar ɗaliban jihar suka zana, wanda wannan yanayi ya jawo wa ɗaliban da suka kammala Jami’o’i rashin zuwa yi wa ƙasa hidima na NYSC saboda rashin sakamakon na WAEC a hannun su.

Sanarwar ta Idris ta ƙara da bayyana cewa, a wancan zaman, an cimma matsaya tsakanin gwamnatin jihar Zamfara da Hukumar ta WAEC kan yadda za a shawo kan lamarin bashin.

“A ƙarshen zaman, Hukumar ta amince za ta fitar da sakamakon jarabawar da suka gabata, tare da amincewa ɗaliban jihar za su zauna don zana jarabawar WAEC ta shekarar 2024.

“Duk ɓangarorin byu sun amince da tsarin da aka yi na biyan bashin da ake bi, tare da cewa za a saki sakamakon jarabawar kafin ƙarshen watannan.”

A wannan ganawa dai, akwai manyan ma’aikatan Hukumar, waɗanda suka haɗa da Mr Ambrose Okelezo, shugaban shiyya; Mr Victor C. Odu, Daraktan kuɗi; da Mr Segun U. Jerumeh, Mataimakin Darakta.

Gwamna Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Tinubu Ya Isa Birnin New York Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya A Karo Na Farko

Tinubu Zai Halarci Taron AU Karo Na 37 A Birnin Addis Ababa Na Kasar Habasha

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.