• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Rahoton Aiki Mai Burgewa

by Sulaiman
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wani Rahoton Aiki Mai Burgewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahoton da babban sakataren jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) Xi Jinping ya gabatar a jiya Lahadi, a yayin bude babban taron wakilan JKS karo na 20 yana da burgewa sosai, saboda cike yake da bayanai masu nasaba da tunanin dora muhimmanci kan moriyar jama’a.

A cikin rahoton, yayin da ake bayyana nasarorin da jam’iyyar ta cimma a shekarun baya, an fi dora mihimmanci kan yadda ta kare rayuka da lafiyar al’umma daga cutar COVID-19, da kawar da talauci a kasar Sin, da kafa tsarin ilimi, da aikin lafiya, da ba da tabbaci ga ingancin zaman rayuwar jama’a mafi girma a duniya.

  • Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

Kana a bangaren ayyukan da za a yi a nan gaba, an jaddada bukatar daidaita matsalolin da suka fi damun jama’a, da samar da isassun damammakin raya kai.

Ban da bayanan rahoton, wasu wakilan JKS mahalartar taron, su ma sun shaidawa manema labaru, yadda tunanin dora muhimmanci kan moriyar jama’a yake yin amfani a kasar.

Zulyati Simayi, wakiliyar JKS ce da ta zo daga jihar Xinjiang ta kasar Sin. Ta yi bayani kan labarin wata yarinya ‘yar Uygur: Wannan yarinya da aka haifa a gundumar Wensu ta garin Aksu, bayan da ta kammala karatun sakandare, ta shiga makarantar koyar da ilimin sana’a, inda ta koyi fasahar hannu ta dinki domin kawata tufafi.

Labarai Masu Nasaba

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Daga baya ta fara aiki a ma’aikatar samar da tufafi don neman inganta fasaharta ta dinki. Zuwa yanzu, bisa tallafin gwamnati, ta kafa wata ma’aikatar dinkin tufafi ta kanta, inda ta samar da dimbin guraben aikin yi ga matasa.

A nata bangare, Jiang Lijuan, matar dake rike da mukamin dagacin kauyen Xiajiang dake lardin Zhejiang na kasar Sin, ta yi bayani kan yadda mutanen kauyenta suke ta cimma burin samun karin kudin shiga.

Ta ce a shekarar 2021, kudin shigar duk mutum daya a tsawon shekara a kauyenta ya kai dalar Amurka 6,522, jimillar da ta ninka ta shekarar 2003 har sau 14. Wannan lamari ya nuna yadda jam’iyyar mai rike da ragamar mulki a kasar Sin, wato JKS, take kokarin sanya ci gaban tattalin arzikin kasar a matsayin abun da zai amfani kowanne mutum na kasar.

Ko shakka babu, yadda ake mai da hankali kan moriyar jama’a, ya sa kasar ta Sin ta dora muhimmanci kan makomar bai daya ta daukacin bil Adama, ta fuskar manufar huldar kasa da kasa ta kasar. Wannan tunani shi ma yana cikin rahoton JKS dake kan karagar mulki a kasar.

A cewar Lin Zhanxi, wakilin JKS, kuma kwararre a fannin nazarin fasahohin aikin gona, shi da tawagarsa na kokarin yayata fasahar noman laimar kwado a duniya, bisa goyon bayan da gwamnatin kasar Sin ta ba su.

Dalilin da ya sa ake yin haka, shi ne wannan fasaha ta taka muhimmiyar rawa, a kokarin kasar Sin na fid da manoma daga kangin talauci. Yanzu haka an horar da ma’aikata fiye da 12,000 a kasashe masu tasowa da dama, wadanda suka yada fasahar zuwa wasu kasashe da yankuna 106.

Ta wadannan misalai, ana iya ganin yadda JKS take kokarin kare moriyar jama’ar kasar Sin, gami da ta dukkan dan Adam, bisa babbar manufarta ta kokarin bautawa jama’a.

Wannan manufar ita ce dalilin da ya sa ta samu damar rike ragamar mulki a kasar Sin har tsawon shekaru 73, kuma take ci gaba da samun goyon baya daga al’ummar kasar Sin. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Da Aka Kai Kan Magoya Bayan PDP A Jihar Kaduna

Next Post

Jami’ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

Related

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

30 minutes ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

2 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

3 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

4 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

22 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

23 hours ago
Next Post
Jami’ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

Jami'ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.