ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Rahoton Aiki Mai Burgewa

by Sulaiman
4 years ago
JKS

Rahoton da babban sakataren jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) Xi Jinping ya gabatar a jiya Lahadi, a yayin bude babban taron wakilan JKS karo na 20 yana da burgewa sosai, saboda cike yake da bayanai masu nasaba da tunanin dora muhimmanci kan moriyar jama’a.

A cikin rahoton, yayin da ake bayyana nasarorin da jam’iyyar ta cimma a shekarun baya, an fi dora mihimmanci kan yadda ta kare rayuka da lafiyar al’umma daga cutar COVID-19, da kawar da talauci a kasar Sin, da kafa tsarin ilimi, da aikin lafiya, da ba da tabbaci ga ingancin zaman rayuwar jama’a mafi girma a duniya.

  • Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

Kana a bangaren ayyukan da za a yi a nan gaba, an jaddada bukatar daidaita matsalolin da suka fi damun jama’a, da samar da isassun damammakin raya kai.

ADVERTISEMENT

Ban da bayanan rahoton, wasu wakilan JKS mahalartar taron, su ma sun shaidawa manema labaru, yadda tunanin dora muhimmanci kan moriyar jama’a yake yin amfani a kasar.

Zulyati Simayi, wakiliyar JKS ce da ta zo daga jihar Xinjiang ta kasar Sin. Ta yi bayani kan labarin wata yarinya ‘yar Uygur: Wannan yarinya da aka haifa a gundumar Wensu ta garin Aksu, bayan da ta kammala karatun sakandare, ta shiga makarantar koyar da ilimin sana’a, inda ta koyi fasahar hannu ta dinki domin kawata tufafi.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Daga baya ta fara aiki a ma’aikatar samar da tufafi don neman inganta fasaharta ta dinki. Zuwa yanzu, bisa tallafin gwamnati, ta kafa wata ma’aikatar dinkin tufafi ta kanta, inda ta samar da dimbin guraben aikin yi ga matasa.

A nata bangare, Jiang Lijuan, matar dake rike da mukamin dagacin kauyen Xiajiang dake lardin Zhejiang na kasar Sin, ta yi bayani kan yadda mutanen kauyenta suke ta cimma burin samun karin kudin shiga.

Ta ce a shekarar 2021, kudin shigar duk mutum daya a tsawon shekara a kauyenta ya kai dalar Amurka 6,522, jimillar da ta ninka ta shekarar 2003 har sau 14. Wannan lamari ya nuna yadda jam’iyyar mai rike da ragamar mulki a kasar Sin, wato JKS, take kokarin sanya ci gaban tattalin arzikin kasar a matsayin abun da zai amfani kowanne mutum na kasar.

Ko shakka babu, yadda ake mai da hankali kan moriyar jama’a, ya sa kasar ta Sin ta dora muhimmanci kan makomar bai daya ta daukacin bil Adama, ta fuskar manufar huldar kasa da kasa ta kasar. Wannan tunani shi ma yana cikin rahoton JKS dake kan karagar mulki a kasar.

A cewar Lin Zhanxi, wakilin JKS, kuma kwararre a fannin nazarin fasahohin aikin gona, shi da tawagarsa na kokarin yayata fasahar noman laimar kwado a duniya, bisa goyon bayan da gwamnatin kasar Sin ta ba su.

Dalilin da ya sa ake yin haka, shi ne wannan fasaha ta taka muhimmiyar rawa, a kokarin kasar Sin na fid da manoma daga kangin talauci. Yanzu haka an horar da ma’aikata fiye da 12,000 a kasashe masu tasowa da dama, wadanda suka yada fasahar zuwa wasu kasashe da yankuna 106.

Ta wadannan misalai, ana iya ganin yadda JKS take kokarin kare moriyar jama’ar kasar Sin, gami da ta dukkan dan Adam, bisa babbar manufarta ta kokarin bautawa jama’a.

Wannan manufar ita ce dalilin da ya sa ta samu damar rike ragamar mulki a kasar Sin har tsawon shekaru 73, kuma take ci gaba da samun goyon baya daga al’ummar kasar Sin. (Bello Wang)

JKS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Jami’ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

Jami'ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.