ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Rahoton Aiki Mai Burgewa

by Sulaiman
4 years ago
JKS

Rahoton da babban sakataren jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin (JKS) Xi Jinping ya gabatar a jiya Lahadi, a yayin bude babban taron wakilan JKS karo na 20 yana da burgewa sosai, saboda cike yake da bayanai masu nasaba da tunanin dora muhimmanci kan moriyar jama’a.

A cikin rahoton, yayin da ake bayyana nasarorin da jam’iyyar ta cimma a shekarun baya, an fi dora mihimmanci kan yadda ta kare rayuka da lafiyar al’umma daga cutar COVID-19, da kawar da talauci a kasar Sin, da kafa tsarin ilimi, da aikin lafiya, da ba da tabbaci ga ingancin zaman rayuwar jama’a mafi girma a duniya.

  • Yadda Kauyen Xiaoheifa Ke Kokarin Rungumar Kyakkyawar Makomarsa A Kasar Sin

Kana a bangaren ayyukan da za a yi a nan gaba, an jaddada bukatar daidaita matsalolin da suka fi damun jama’a, da samar da isassun damammakin raya kai.

ADVERTISEMENT

Ban da bayanan rahoton, wasu wakilan JKS mahalartar taron, su ma sun shaidawa manema labaru, yadda tunanin dora muhimmanci kan moriyar jama’a yake yin amfani a kasar.

Zulyati Simayi, wakiliyar JKS ce da ta zo daga jihar Xinjiang ta kasar Sin. Ta yi bayani kan labarin wata yarinya ‘yar Uygur: Wannan yarinya da aka haifa a gundumar Wensu ta garin Aksu, bayan da ta kammala karatun sakandare, ta shiga makarantar koyar da ilimin sana’a, inda ta koyi fasahar hannu ta dinki domin kawata tufafi.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Daga baya ta fara aiki a ma’aikatar samar da tufafi don neman inganta fasaharta ta dinki. Zuwa yanzu, bisa tallafin gwamnati, ta kafa wata ma’aikatar dinkin tufafi ta kanta, inda ta samar da dimbin guraben aikin yi ga matasa.

A nata bangare, Jiang Lijuan, matar dake rike da mukamin dagacin kauyen Xiajiang dake lardin Zhejiang na kasar Sin, ta yi bayani kan yadda mutanen kauyenta suke ta cimma burin samun karin kudin shiga.

Ta ce a shekarar 2021, kudin shigar duk mutum daya a tsawon shekara a kauyenta ya kai dalar Amurka 6,522, jimillar da ta ninka ta shekarar 2003 har sau 14. Wannan lamari ya nuna yadda jam’iyyar mai rike da ragamar mulki a kasar Sin, wato JKS, take kokarin sanya ci gaban tattalin arzikin kasar a matsayin abun da zai amfani kowanne mutum na kasar.

Ko shakka babu, yadda ake mai da hankali kan moriyar jama’a, ya sa kasar ta Sin ta dora muhimmanci kan makomar bai daya ta daukacin bil Adama, ta fuskar manufar huldar kasa da kasa ta kasar. Wannan tunani shi ma yana cikin rahoton JKS dake kan karagar mulki a kasar.

A cewar Lin Zhanxi, wakilin JKS, kuma kwararre a fannin nazarin fasahohin aikin gona, shi da tawagarsa na kokarin yayata fasahar noman laimar kwado a duniya, bisa goyon bayan da gwamnatin kasar Sin ta ba su.

Dalilin da ya sa ake yin haka, shi ne wannan fasaha ta taka muhimmiyar rawa, a kokarin kasar Sin na fid da manoma daga kangin talauci. Yanzu haka an horar da ma’aikata fiye da 12,000 a kasashe masu tasowa da dama, wadanda suka yada fasahar zuwa wasu kasashe da yankuna 106.

Ta wadannan misalai, ana iya ganin yadda JKS take kokarin kare moriyar jama’ar kasar Sin, gami da ta dukkan dan Adam, bisa babbar manufarta ta kokarin bautawa jama’a.

Wannan manufar ita ce dalilin da ya sa ta samu damar rike ragamar mulki a kasar Sin har tsawon shekaru 73, kuma take ci gaba da samun goyon baya daga al’ummar kasar Sin. (Bello Wang)

JKS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu
  • Sulaiman
    Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

MASU ALAKA

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Next Post
Jami’ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

Jami'ar Bayero Ta Sanar Da Ranar Bude Makaranta Don Ci Gaba Da Karatu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

June 15, 2026
Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.