• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai wani zancen hikima, dake yaduwa a wasu sassan nahiyar Afirka, wanda ma’anarsa ita ce, “A yankin fako a kan samu mutane masu fama da talauci, kana mutanen su ma suna kara fadada wuraren fako.” Wannan magana ta nuna mawuyacin halin da ake fama da shi a wurare masu kusa da yankin hamada, inda ake samun tabarbarewar yanayin talauci, da matsalar sarrafa albarkatu ba bisa ka’ida ba, da lalacewar muhallin halittu, bisa yadda wadannan matsalolin suke wa juna tasiri. Sai dai yanzu an samu damar daidaita wannan yanayi mai wuya, bisa karfafar hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka.

A yau ne na karanta wani bayanin da ya shafi ci gaban aikin gina yankin nuna fasahohin kyautata muhallin halittu na Sin da Afirka, da ake gudanar da shi a kasar Mauritania. An ce, wasu kwararru ‘yan kasar Sin sun gina wani “yankin dausayi” a cikin yankin kasar dake dab da hamadar Sahara, inda suka nuna fasahohin hana kwararar hamada, da tsimin ruwa, da daidaita yanayin kasa don biyan bukatar gudanar da aikin gona, da samar da kayan lambu mai jure yanayin karancin ruwa, da saka na’urorin zamani na ban ruwa ta wutar lantarki da ake samu daga zafin hasken rana, da wadanda ke iya sarrafa kansu wajen samar da ruwa ga kayayyakin gona, da dai sauransu.

Hakika kasar Sin ta kware a fannin daidaita matsalar kwararar hamada, inda ta cika burin dakatar da yanayin lalacewar kasa da Majalisar Dinkin Duniya ta sanya, wasu shekaru 10 kafin lokacin da aka kayyade. Daga baya, kasar ta yi amfani da fasahohinta wajen tallafa wa shirin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU ta gabatar na gina “babban shingen itatuwa” a nahiyar Afirka, ta yadda aka rage fadin yankuna masu fama da matsalar kwararar hamada daga kaso 72.31% zuwa 69.23% a yankin Sahel dake Afirka, tsakanin shekarar 2000 da ta 2020.

Yanzu a jihar Kano ta Najeriya, wata cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka ta kafa yankin nuna fasahohin hana kwararowar hamada, da na dasa itatuwa masu samar da riba, a kokarin daidaita wasu matsalolin da ake fuskantar, da suka hada da habakar yankin hamada, da raguwar karfin kasa a fannin biyan bukatar aikin gona, da karancin ciyayi, da na ruwa, da dai sauransu.

Wasu mutane su kan yi shakku game da hadin gwiwar da ake yi tsakanin bangarorin Sin da Afirka, inda su kan ce wai “kasar Sin ta fi samun moriya.” Sai dai ya kamata a dubi yadda wadannan kwararru Sinawa suka shiga cikin yankunan hamada na kasashen Afirka, tare da samar da gudunmowa a can. To, mece ce moriyar da suke nema daga aikin?

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Hakika abin da suke yi shi ne kokarin cika alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta sanya, na taimakon yankunan karkara na kasashen Afirka wajen samun hakikanin ci gaba, inda za a kyautata muhallin rayuwar mutane, da fitar da su daga kangin talauci, maimakon samar da karuwar adadin tattalin arziki kawai.

Kana a bayan manufar ta kasar Sin akwai wani tunani mai muhimmanci da kasar ta rike, wato na “Gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”. A ganin kasar Sin, dukkan al’ummun kasashe daban daban suna zama a duniya daya, don haka suna da makomar bai daya. Saboda haka ya kamata a lura da bukatun sauran kasashe, da tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai daya, yayin da wata kasa ke neman raya kanta. To, yanzu mun ga yadda wannan tunani ya shafa launin kore kan hamadar Sahara, kuma tabbas zai haifar da karin ci gaba ga nahiyar Afirka a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallah Babba Tare Da Malta Guinness A Kano

Next Post

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Related

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

3 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

2 days ago
Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

1 week ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

2 weeks ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

3 weeks ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

3 weeks ago
Next Post
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.