• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai wani zancen hikima, dake yaduwa a wasu sassan nahiyar Afirka, wanda ma’anarsa ita ce, “A yankin fako a kan samu mutane masu fama da talauci, kana mutanen su ma suna kara fadada wuraren fako.” Wannan magana ta nuna mawuyacin halin da ake fama da shi a wurare masu kusa da yankin hamada, inda ake samun tabarbarewar yanayin talauci, da matsalar sarrafa albarkatu ba bisa ka’ida ba, da lalacewar muhallin halittu, bisa yadda wadannan matsalolin suke wa juna tasiri. Sai dai yanzu an samu damar daidaita wannan yanayi mai wuya, bisa karfafar hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka.

A yau ne na karanta wani bayanin da ya shafi ci gaban aikin gina yankin nuna fasahohin kyautata muhallin halittu na Sin da Afirka, da ake gudanar da shi a kasar Mauritania. An ce, wasu kwararru ‘yan kasar Sin sun gina wani “yankin dausayi” a cikin yankin kasar dake dab da hamadar Sahara, inda suka nuna fasahohin hana kwararar hamada, da tsimin ruwa, da daidaita yanayin kasa don biyan bukatar gudanar da aikin gona, da samar da kayan lambu mai jure yanayin karancin ruwa, da saka na’urorin zamani na ban ruwa ta wutar lantarki da ake samu daga zafin hasken rana, da wadanda ke iya sarrafa kansu wajen samar da ruwa ga kayayyakin gona, da dai sauransu.

Hakika kasar Sin ta kware a fannin daidaita matsalar kwararar hamada, inda ta cika burin dakatar da yanayin lalacewar kasa da Majalisar Dinkin Duniya ta sanya, wasu shekaru 10 kafin lokacin da aka kayyade. Daga baya, kasar ta yi amfani da fasahohinta wajen tallafa wa shirin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU ta gabatar na gina “babban shingen itatuwa” a nahiyar Afirka, ta yadda aka rage fadin yankuna masu fama da matsalar kwararar hamada daga kaso 72.31% zuwa 69.23% a yankin Sahel dake Afirka, tsakanin shekarar 2000 da ta 2020.

Yanzu a jihar Kano ta Najeriya, wata cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka ta kafa yankin nuna fasahohin hana kwararowar hamada, da na dasa itatuwa masu samar da riba, a kokarin daidaita wasu matsalolin da ake fuskantar, da suka hada da habakar yankin hamada, da raguwar karfin kasa a fannin biyan bukatar aikin gona, da karancin ciyayi, da na ruwa, da dai sauransu.

Wasu mutane su kan yi shakku game da hadin gwiwar da ake yi tsakanin bangarorin Sin da Afirka, inda su kan ce wai “kasar Sin ta fi samun moriya.” Sai dai ya kamata a dubi yadda wadannan kwararru Sinawa suka shiga cikin yankunan hamada na kasashen Afirka, tare da samar da gudunmowa a can. To, mece ce moriyar da suke nema daga aikin?

Labarai Masu Nasaba

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Hakika abin da suke yi shi ne kokarin cika alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta sanya, na taimakon yankunan karkara na kasashen Afirka wajen samun hakikanin ci gaba, inda za a kyautata muhallin rayuwar mutane, da fitar da su daga kangin talauci, maimakon samar da karuwar adadin tattalin arziki kawai.

Kana a bayan manufar ta kasar Sin akwai wani tunani mai muhimmanci da kasar ta rike, wato na “Gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”. A ganin kasar Sin, dukkan al’ummun kasashe daban daban suna zama a duniya daya, don haka suna da makomar bai daya. Saboda haka ya kamata a lura da bukatun sauran kasashe, da tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai daya, yayin da wata kasa ke neman raya kanta. To, yanzu mun ga yadda wannan tunani ya shafa launin kore kan hamadar Sahara, kuma tabbas zai haifar da karin ci gaba ga nahiyar Afirka a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallah Babba Tare Da Malta Guinness A Kano

Next Post

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Related

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

22 hours ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

5 days ago
Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna
Ra'ayi Riga

Guguwa Za Ta Sa Kasashen Sin Da Afirka Su Kara Rike Hannayen Juna

1 week ago
Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka
Ra'ayi Riga

Ba Mu Iya “Gina” Ayaba A Amurka

1 week ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

2 weeks ago
Next Post
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.