ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sahara

Akwai wani zancen hikima, dake yaduwa a wasu sassan nahiyar Afirka, wanda ma’anarsa ita ce, “A yankin fako a kan samu mutane masu fama da talauci, kana mutanen su ma suna kara fadada wuraren fako.” Wannan magana ta nuna mawuyacin halin da ake fama da shi a wurare masu kusa da yankin hamada, inda ake samun tabarbarewar yanayin talauci, da matsalar sarrafa albarkatu ba bisa ka’ida ba, da lalacewar muhallin halittu, bisa yadda wadannan matsalolin suke wa juna tasiri. Sai dai yanzu an samu damar daidaita wannan yanayi mai wuya, bisa karfafar hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka.

A yau ne na karanta wani bayanin da ya shafi ci gaban aikin gina yankin nuna fasahohin kyautata muhallin halittu na Sin da Afirka, da ake gudanar da shi a kasar Mauritania. An ce, wasu kwararru ‘yan kasar Sin sun gina wani “yankin dausayi” a cikin yankin kasar dake dab da hamadar Sahara, inda suka nuna fasahohin hana kwararar hamada, da tsimin ruwa, da daidaita yanayin kasa don biyan bukatar gudanar da aikin gona, da samar da kayan lambu mai jure yanayin karancin ruwa, da saka na’urorin zamani na ban ruwa ta wutar lantarki da ake samu daga zafin hasken rana, da wadanda ke iya sarrafa kansu wajen samar da ruwa ga kayayyakin gona, da dai sauransu.

Hakika kasar Sin ta kware a fannin daidaita matsalar kwararar hamada, inda ta cika burin dakatar da yanayin lalacewar kasa da Majalisar Dinkin Duniya ta sanya, wasu shekaru 10 kafin lokacin da aka kayyade. Daga baya, kasar ta yi amfani da fasahohinta wajen tallafa wa shirin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU ta gabatar na gina “babban shingen itatuwa” a nahiyar Afirka, ta yadda aka rage fadin yankuna masu fama da matsalar kwararar hamada daga kaso 72.31% zuwa 69.23% a yankin Sahel dake Afirka, tsakanin shekarar 2000 da ta 2020.

ADVERTISEMENT

Yanzu a jihar Kano ta Najeriya, wata cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka ta kafa yankin nuna fasahohin hana kwararowar hamada, da na dasa itatuwa masu samar da riba, a kokarin daidaita wasu matsalolin da ake fuskantar, da suka hada da habakar yankin hamada, da raguwar karfin kasa a fannin biyan bukatar aikin gona, da karancin ciyayi, da na ruwa, da dai sauransu.

Wasu mutane su kan yi shakku game da hadin gwiwar da ake yi tsakanin bangarorin Sin da Afirka, inda su kan ce wai “kasar Sin ta fi samun moriya.” Sai dai ya kamata a dubi yadda wadannan kwararru Sinawa suka shiga cikin yankunan hamada na kasashen Afirka, tare da samar da gudunmowa a can. To, mece ce moriyar da suke nema daga aikin?

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Hakika abin da suke yi shi ne kokarin cika alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta sanya, na taimakon yankunan karkara na kasashen Afirka wajen samun hakikanin ci gaba, inda za a kyautata muhallin rayuwar mutane, da fitar da su daga kangin talauci, maimakon samar da karuwar adadin tattalin arziki kawai.

Kana a bayan manufar ta kasar Sin akwai wani tunani mai muhimmanci da kasar ta rike, wato na “Gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”. A ganin kasar Sin, dukkan al’ummun kasashe daban daban suna zama a duniya daya, don haka suna da makomar bai daya. Saboda haka ya kamata a lura da bukatun sauran kasashe, da tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai daya, yayin da wata kasa ke neman raya kanta. To, yanzu mun ga yadda wannan tunani ya shafa launin kore kan hamadar Sahara, kuma tabbas zai haifar da karin ci gaba ga nahiyar Afirka a nan gaba. (Bello Wang)

Sahara
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sahara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.