ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sahara

Akwai wani zancen hikima, dake yaduwa a wasu sassan nahiyar Afirka, wanda ma’anarsa ita ce, “A yankin fako a kan samu mutane masu fama da talauci, kana mutanen su ma suna kara fadada wuraren fako.” Wannan magana ta nuna mawuyacin halin da ake fama da shi a wurare masu kusa da yankin hamada, inda ake samun tabarbarewar yanayin talauci, da matsalar sarrafa albarkatu ba bisa ka’ida ba, da lalacewar muhallin halittu, bisa yadda wadannan matsalolin suke wa juna tasiri. Sai dai yanzu an samu damar daidaita wannan yanayi mai wuya, bisa karfafar hadin gwiwar bangarorin Sin da Afirka.

A yau ne na karanta wani bayanin da ya shafi ci gaban aikin gina yankin nuna fasahohin kyautata muhallin halittu na Sin da Afirka, da ake gudanar da shi a kasar Mauritania. An ce, wasu kwararru ‘yan kasar Sin sun gina wani “yankin dausayi” a cikin yankin kasar dake dab da hamadar Sahara, inda suka nuna fasahohin hana kwararar hamada, da tsimin ruwa, da daidaita yanayin kasa don biyan bukatar gudanar da aikin gona, da samar da kayan lambu mai jure yanayin karancin ruwa, da saka na’urorin zamani na ban ruwa ta wutar lantarki da ake samu daga zafin hasken rana, da wadanda ke iya sarrafa kansu wajen samar da ruwa ga kayayyakin gona, da dai sauransu.

Hakika kasar Sin ta kware a fannin daidaita matsalar kwararar hamada, inda ta cika burin dakatar da yanayin lalacewar kasa da Majalisar Dinkin Duniya ta sanya, wasu shekaru 10 kafin lokacin da aka kayyade. Daga baya, kasar ta yi amfani da fasahohinta wajen tallafa wa shirin da kungiyar tarayyar Afirka ta AU ta gabatar na gina “babban shingen itatuwa” a nahiyar Afirka, ta yadda aka rage fadin yankuna masu fama da matsalar kwararar hamada daga kaso 72.31% zuwa 69.23% a yankin Sahel dake Afirka, tsakanin shekarar 2000 da ta 2020.

ADVERTISEMENT

Yanzu a jihar Kano ta Najeriya, wata cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka ta kafa yankin nuna fasahohin hana kwararowar hamada, da na dasa itatuwa masu samar da riba, a kokarin daidaita wasu matsalolin da ake fuskantar, da suka hada da habakar yankin hamada, da raguwar karfin kasa a fannin biyan bukatar aikin gona, da karancin ciyayi, da na ruwa, da dai sauransu.

Wasu mutane su kan yi shakku game da hadin gwiwar da ake yi tsakanin bangarorin Sin da Afirka, inda su kan ce wai “kasar Sin ta fi samun moriya.” Sai dai ya kamata a dubi yadda wadannan kwararru Sinawa suka shiga cikin yankunan hamada na kasashen Afirka, tare da samar da gudunmowa a can. To, mece ce moriyar da suke nema daga aikin?

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Hakika abin da suke yi shi ne kokarin cika alkawarin da gwamnatin kasar Sin ta sanya, na taimakon yankunan karkara na kasashen Afirka wajen samun hakikanin ci gaba, inda za a kyautata muhallin rayuwar mutane, da fitar da su daga kangin talauci, maimakon samar da karuwar adadin tattalin arziki kawai.

Kana a bayan manufar ta kasar Sin akwai wani tunani mai muhimmanci da kasar ta rike, wato na “Gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya”. A ganin kasar Sin, dukkan al’ummun kasashe daban daban suna zama a duniya daya, don haka suna da makomar bai daya. Saboda haka ya kamata a lura da bukatun sauran kasashe, da tabbatar da ci gaban mabambantan kasashe na bai daya, yayin da wata kasa ke neman raya kanta. To, yanzu mun ga yadda wannan tunani ya shafa launin kore kan hamadar Sahara, kuma tabbas zai haifar da karin ci gaba ga nahiyar Afirka a nan gaba. (Bello Wang)

Sahara
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela
Sahara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas
  • Sulaiman
    Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Next Post
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

LABARAI MASU NASABA

'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.