• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alkaluman baya bayan nan da kafofin watsa labarai ke fitarwa na nuna cewa, tuni adadin mutane da suka rasu, sakamakon dauki-ba-dadin dake aukuwa tsakanin sojojin Isra’ila da mayakan kungiyar Hamas sun haura 2,200 tare da jikkata wasu 8,000, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

Mafi yawan masu fashin baki dai na cewa, yakin na wannan karo bai zo da mamaki ba, duba da har yanzu ba a kai ga cimma managarcin tsarin warware rikicin Isra’ila da Falasdinawa yadda ya kamata ba.

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar Da Matasa ‘Yan Sa-Kai
  • Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Kasashe irin su Sin da masu ra’ayi irin nata, sun sha nanata bukatar kawo karshen wannan takaddama ta hanyar siyasa, wato hawan teburin shawara, da ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, wadanda za su baiwa Isra’ilawa da Falasdinawa damar zama da juna lami lafiya, kuma cikin ’yanci. To amma sabanin hakan, wasu daga kasashen yamma, sun ki baiwa wadannan shawarwari goyon bayan da ya dace, ko da a matsayinsu na daidaikun kasashe kawayen Isra’ila, ko kuma a dandalin kasa da kasa kamar na MDD.

Shaidar dake tabbatar da hakan ita ce yadda a ranar Talata, shugaban Amurka Joe Biden ya ayyana mika taimakon kayayyakin aikin soji ga Isra’ila, da nufin tallafa mata wajen murkushe hare-haren da Hamas ke kaddamarwa kan yankunanta, ko da yake shugaban na Amurka ya ce bai dace wata kasa ta yi amfani da sabon fadan da ya barke da nufin cimma wani buri na kashin kai ba.

Idan mun yi nazari da kyau, za mu ga cewa, Amurka ba ta sauya daga matsayarta ta raba kafa ba, domin kuwa idan har ba ta da burin amfani da wannan yaki a matsayin wata dama ta cimma burin kashin kai kamar yadda shugaba Biden ya ambata, to bai kamata ta yi gaggawar aikewa Isra’ila da kayan yaki ba, maimakon haka, kamata ya yi ta shige gaba wajen tabbatar da an tsagaita wuta, da kai zuciya nesa, tare da jan hankalin sassan biyu ga bukatar komawa shawarwari.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Bugu da kari, ya kamata Amurka, da sauran kasashen yamma irin su Jamus da Faransa, wadanda suka fito fili wajen bayyana takaicinsu ga sake barkewar fada, su waiwayi baya, su san cewa “Zama lafiya ya fi zama dan sarki”, su kuma goyi bayan kafuwar kasashe biyu a matsayin mataki mafi dacewa, na kawo karshen takaddamar Isra’ila da Falasdina bisa adalci, idan kuwa suka ki rungumar wannan shawara, to ko shakka babu duniya za ta ci gaba da kallon su a matsayin masu “Fakewa da guzuma domin harbin karsana”. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuIsra'ilaZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Yi Rangadi A Biranen Jingdezhen Da Shangrao Na Lardin Jiangxi 

Next Post

Jakadan Kofi Na Ruwanda

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

14 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

14 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

16 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

19 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Jakadan Kofi Na Ruwanda

Jakadan Kofi Na Ruwanda

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.