• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alkaluman baya bayan nan da kafofin watsa labarai ke fitarwa na nuna cewa, tuni adadin mutane da suka rasu, sakamakon dauki-ba-dadin dake aukuwa tsakanin sojojin Isra’ila da mayakan kungiyar Hamas sun haura 2,200 tare da jikkata wasu 8,000, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

Mafi yawan masu fashin baki dai na cewa, yakin na wannan karo bai zo da mamaki ba, duba da har yanzu ba a kai ga cimma managarcin tsarin warware rikicin Isra’ila da Falasdinawa yadda ya kamata ba.

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar Da Matasa ‘Yan Sa-Kai
  • Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Kasashe irin su Sin da masu ra’ayi irin nata, sun sha nanata bukatar kawo karshen wannan takaddama ta hanyar siyasa, wato hawan teburin shawara, da ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, wadanda za su baiwa Isra’ilawa da Falasdinawa damar zama da juna lami lafiya, kuma cikin ’yanci. To amma sabanin hakan, wasu daga kasashen yamma, sun ki baiwa wadannan shawarwari goyon bayan da ya dace, ko da a matsayinsu na daidaikun kasashe kawayen Isra’ila, ko kuma a dandalin kasa da kasa kamar na MDD.

Shaidar dake tabbatar da hakan ita ce yadda a ranar Talata, shugaban Amurka Joe Biden ya ayyana mika taimakon kayayyakin aikin soji ga Isra’ila, da nufin tallafa mata wajen murkushe hare-haren da Hamas ke kaddamarwa kan yankunanta, ko da yake shugaban na Amurka ya ce bai dace wata kasa ta yi amfani da sabon fadan da ya barke da nufin cimma wani buri na kashin kai ba.

Idan mun yi nazari da kyau, za mu ga cewa, Amurka ba ta sauya daga matsayarta ta raba kafa ba, domin kuwa idan har ba ta da burin amfani da wannan yaki a matsayin wata dama ta cimma burin kashin kai kamar yadda shugaba Biden ya ambata, to bai kamata ta yi gaggawar aikewa Isra’ila da kayan yaki ba, maimakon haka, kamata ya yi ta shige gaba wajen tabbatar da an tsagaita wuta, da kai zuciya nesa, tare da jan hankalin sassan biyu ga bukatar komawa shawarwari.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Bugu da kari, ya kamata Amurka, da sauran kasashen yamma irin su Jamus da Faransa, wadanda suka fito fili wajen bayyana takaicinsu ga sake barkewar fada, su waiwayi baya, su san cewa “Zama lafiya ya fi zama dan sarki”, su kuma goyi bayan kafuwar kasashe biyu a matsayin mataki mafi dacewa, na kawo karshen takaddamar Isra’ila da Falasdina bisa adalci, idan kuwa suka ki rungumar wannan shawara, to ko shakka babu duniya za ta ci gaba da kallon su a matsayin masu “Fakewa da guzuma domin harbin karsana”. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuIsra'ilaZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Yi Rangadi A Biranen Jingdezhen Da Shangrao Na Lardin Jiangxi 

Next Post

Jakadan Kofi Na Ruwanda

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

15 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

16 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

17 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

18 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

19 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
Jakadan Kofi Na Ruwanda

Jakadan Kofi Na Ruwanda

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.