• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alkaluman baya bayan nan da kafofin watsa labarai ke fitarwa na nuna cewa, tuni adadin mutane da suka rasu, sakamakon dauki-ba-dadin dake aukuwa tsakanin sojojin Isra’ila da mayakan kungiyar Hamas sun haura 2,200 tare da jikkata wasu 8,000, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

Mafi yawan masu fashin baki dai na cewa, yakin na wannan karo bai zo da mamaki ba, duba da har yanzu ba a kai ga cimma managarcin tsarin warware rikicin Isra’ila da Falasdinawa yadda ya kamata ba.

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar Da Matasa ‘Yan Sa-Kai
  • Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Kasashe irin su Sin da masu ra’ayi irin nata, sun sha nanata bukatar kawo karshen wannan takaddama ta hanyar siyasa, wato hawan teburin shawara, da ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, wadanda za su baiwa Isra’ilawa da Falasdinawa damar zama da juna lami lafiya, kuma cikin ’yanci. To amma sabanin hakan, wasu daga kasashen yamma, sun ki baiwa wadannan shawarwari goyon bayan da ya dace, ko da a matsayinsu na daidaikun kasashe kawayen Isra’ila, ko kuma a dandalin kasa da kasa kamar na MDD.

Shaidar dake tabbatar da hakan ita ce yadda a ranar Talata, shugaban Amurka Joe Biden ya ayyana mika taimakon kayayyakin aikin soji ga Isra’ila, da nufin tallafa mata wajen murkushe hare-haren da Hamas ke kaddamarwa kan yankunanta, ko da yake shugaban na Amurka ya ce bai dace wata kasa ta yi amfani da sabon fadan da ya barke da nufin cimma wani buri na kashin kai ba.

Idan mun yi nazari da kyau, za mu ga cewa, Amurka ba ta sauya daga matsayarta ta raba kafa ba, domin kuwa idan har ba ta da burin amfani da wannan yaki a matsayin wata dama ta cimma burin kashin kai kamar yadda shugaba Biden ya ambata, to bai kamata ta yi gaggawar aikewa Isra’ila da kayan yaki ba, maimakon haka, kamata ya yi ta shige gaba wajen tabbatar da an tsagaita wuta, da kai zuciya nesa, tare da jan hankalin sassan biyu ga bukatar komawa shawarwari.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Bugu da kari, ya kamata Amurka, da sauran kasashen yamma irin su Jamus da Faransa, wadanda suka fito fili wajen bayyana takaicinsu ga sake barkewar fada, su waiwayi baya, su san cewa “Zama lafiya ya fi zama dan sarki”, su kuma goyi bayan kafuwar kasashe biyu a matsayin mataki mafi dacewa, na kawo karshen takaddamar Isra’ila da Falasdina bisa adalci, idan kuwa suka ki rungumar wannan shawara, to ko shakka babu duniya za ta ci gaba da kallon su a matsayin masu “Fakewa da guzuma domin harbin karsana”. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuIsra'ilaZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Yi Rangadi A Biranen Jingdezhen Da Shangrao Na Lardin Jiangxi 

Next Post

Jakadan Kofi Na Ruwanda

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

6 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

7 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

8 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

9 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

10 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

11 hours ago
Next Post
Jakadan Kofi Na Ruwanda

Jakadan Kofi Na Ruwanda

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.