ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wanzar Da Zaman Lafiya Ne Babban Aikin Da Ya Dace A Sanya Gaba A Gabas Ta Tsakiya

by CGTN Hausa
3 years ago
Zaman lafiya

Alkaluman baya bayan nan da kafofin watsa labarai ke fitarwa na nuna cewa, tuni adadin mutane da suka rasu, sakamakon dauki-ba-dadin dake aukuwa tsakanin sojojin Isra’ila da mayakan kungiyar Hamas sun haura 2,200 tare da jikkata wasu 8,000, tun bayan barkewar fada a ranar Asabar.

Mafi yawan masu fashin baki dai na cewa, yakin na wannan karo bai zo da mamaki ba, duba da har yanzu ba a kai ga cimma managarcin tsarin warware rikicin Isra’ila da Falasdinawa yadda ya kamata ba.

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar Da Matasa ‘Yan Sa-Kai
  • Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Kasashe irin su Sin da masu ra’ayi irin nata, sun sha nanata bukatar kawo karshen wannan takaddama ta hanyar siyasa, wato hawan teburin shawara, da ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kansu, wadanda za su baiwa Isra’ilawa da Falasdinawa damar zama da juna lami lafiya, kuma cikin ’yanci. To amma sabanin hakan, wasu daga kasashen yamma, sun ki baiwa wadannan shawarwari goyon bayan da ya dace, ko da a matsayinsu na daidaikun kasashe kawayen Isra’ila, ko kuma a dandalin kasa da kasa kamar na MDD.

ADVERTISEMENT

Shaidar dake tabbatar da hakan ita ce yadda a ranar Talata, shugaban Amurka Joe Biden ya ayyana mika taimakon kayayyakin aikin soji ga Isra’ila, da nufin tallafa mata wajen murkushe hare-haren da Hamas ke kaddamarwa kan yankunanta, ko da yake shugaban na Amurka ya ce bai dace wata kasa ta yi amfani da sabon fadan da ya barke da nufin cimma wani buri na kashin kai ba.

Idan mun yi nazari da kyau, za mu ga cewa, Amurka ba ta sauya daga matsayarta ta raba kafa ba, domin kuwa idan har ba ta da burin amfani da wannan yaki a matsayin wata dama ta cimma burin kashin kai kamar yadda shugaba Biden ya ambata, to bai kamata ta yi gaggawar aikewa Isra’ila da kayan yaki ba, maimakon haka, kamata ya yi ta shige gaba wajen tabbatar da an tsagaita wuta, da kai zuciya nesa, tare da jan hankalin sassan biyu ga bukatar komawa shawarwari.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Bugu da kari, ya kamata Amurka, da sauran kasashen yamma irin su Jamus da Faransa, wadanda suka fito fili wajen bayyana takaicinsu ga sake barkewar fada, su waiwayi baya, su san cewa “Zama lafiya ya fi zama dan sarki”, su kuma goyi bayan kafuwar kasashe biyu a matsayin mataki mafi dacewa, na kawo karshen takaddamar Isra’ila da Falasdina bisa adalci, idan kuwa suka ki rungumar wannan shawara, to ko shakka babu duniya za ta ci gaba da kallon su a matsayin masu “Fakewa da guzuma domin harbin karsana”. (Saminu Alhassan)

Zaman lafiya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”
Daga Birnin Sin

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Next Post
Jakadan Kofi Na Ruwanda

Jakadan Kofi Na Ruwanda

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.