• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

by Rabilu Sanusi Bena
3 months ago
in Wasanni
0
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kocin Paris Saint-Germain (PSG), Luis Enrique, ya bayyana cewa wasan da ƙungiyarsa za ta fafata da Real Madrid a daf da na kusa da ƙarshe na gasar cin kofin Duniya zai kasance “na musamman“. Sai dai Enrique ya kaucewa magana kan tsohon ɗan wasansa, Kylian Mbappé, wanda yanzu ke buga wasa a Real Madrid.

A wani taron manema labarai da aka gudanar a filin wasa na MetLife da ke kusa da birnin New York, Enrique ya ce duk lokacin da aka yi wasa da Real Madrid, wannan wasa ba ƙaramin abu ba ne. Yayin da PSG ke kokarin cigaba da jan zarenta bayan nasararta a kakar bana, Xabi Alonso na Real Madrid shima na fatan lashe kofinsa na farko a matsayin koci.

  • Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi
  • NIS Ta Yi Wa Manyan Jami’ai 98 Ado Da Sabbin Muƙamansu

PSG ta zo gasar da kwarin gwuiwa bayan ta lashe gasar zakarun Turai ta UEFA Champions League a karo na farko a tarihinta. Wasan da za su buga da Real Madrid na zuwa ne bayan tafiyar Mbappé zuwa Madrid, inda Enrique ya horar da shi a kakarsa ta ƙarshe a PSG. Mbappé ya sha fama da ƙin saka hannu kan sabon kwantiragi, wanda ya sa aka dinga dakatar da shi daga buga wasanni a wancan lokaci.

Enrique ya ce, “Wannan wasa na da matuƙar muhimmanci, ba wai kawai saboda suna Real Madrid ba, amma kuma saboda muna kusa da wasan ƙarshe na gasar cin kofin duniya.” Ya ce nasara a wannan wasan zai buɗe musu ƙofar zuwa wasan ƙarshe da zai kasance babban abin alfahari ga ƙungiyar.

Duk wanda ya samu nasara a wasan PSG da Real Madrid zai haɗu da Chelsea a wasan ƙarshe a ranar Lahadi. Chelsea ta samu nasarar doke Fluminense da ci 2-0 a zagaye na huɗu, wanda ya sa ta samu gurbin wasan ƙarshe.

Labarai Masu Nasaba

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MadridPSG
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki

Next Post

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Related

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

10 hours ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

2 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

3 days ago
Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku
Wasanni

Kofin Duniya: FIFA Ta Zabtarewa Afirka Ta Kudu Maki Uku

4 days ago
Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad
Wasanni

Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

5 days ago
Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta
Wasanni

Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

5 days ago
Next Post
Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

Sabbin Gonakin Da Za A Magance Zaizayewar Kasa A Sin A Karshen Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Na 14 Sun Kai Muraba’in Kilomita 340,000

October 3, 2025
Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

Jami’in MDD: Kayataccen Hutun “Golden Week Plus” Na Kasar Sin Ya Nuna Tasirin Yawon Bude Ido A Duniya 

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.