• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Halayen Da Maza Ke Nuna Wa Uwargida In Sun Shirya Kara Aure

byAmina Usman
3 years ago
Maza

Kamar yadda aka sani aure wani nau’i ne na ibada wanda yake haifar da nishadi natsuwa da jin dadi. Idan aka ce aure ana nufin sadaukarwa da kuma girmama juna.

Zamantakewar aure abu ne da aka gina shi a kan abubuwa biyu zuwa uku na farko akwai kishin juna na biyu akwai yarda da amana.

  • Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta
  • LP, Ta Kori Daraktan Yakin Neman Zaben Obi, Okupe Da Wasu 11 Kan Gaza Biyan Harajin Jam’iyyar

Idan muka dauki yarda da amana zamu ga cewa wani abu ne da ma’auratan biyu suka damkawa junansu inda zamu ga cewa miji yana kokarin kare duk wani martaba na matarsa haka itama matar.

Idan muka yi dubi da shimfidan da na fara zamu ga cewa an gina zaman aure a kan turaban sadaukarwa da amana, idan kuwa haka ne to me yasa Miji ke juya wa uwargida baya a lokacin da yake kokarin karo aure?
Yawanci maza in sun yi shirin karin aure gaskiya akwai halayya iri daban-daban da uwargida ke cin karo da su a wurin Maigida ,wanda zamu ga cewa gaba daya miji yakan manta irin zaman dadi da kuma zaman hakuri da ta yi da shi.

Hakazalika miji yana sauyawa ta halayya daban-daban ga uwargida inda har wani lokaci in ba a kai zuciya nesa ba saki ko sabani mai karfi na iya shiga tsakani.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

Yawanci maza in sun zo karin aure sukan sauya fuska da walwala wa uwargida wanda hakan an yi ittifakin cewa yawanci maza suna ganin cewa si yanzu ita uwargida ta ragwaba bata da sauran mamora shiyasa idon su sai ya kyalla ya fara hango musu wata a waje,wanda har zai kai ga ana diban lokacin uwargida ana baiwa amarya tun kafin ta shigo gidan.

Wani lokaci zakaga idan miji ya fara shirin karin aure zai dauko wasu sababbin halayya wanda uwargida bata sansu ba ya dorawa kansa, kamar misali akwai mijin da zakaga idan yaso karin aure to fa uwargida ta shiga uku don komai ta yi ba ta burge shi ba saima hantara da fada da zai dinga yawan yi mata, ko kuma kaga wani mijin in yaso karin aure to ya daina shiga harkan uwargida musamman da muke da kafafen soshiyal media daban-daban to gaba daya lokacin shi ya zama na amarya ko yaushe suna manne a waya ko kuma suna ‘Charting’ ita uwargida an ajiyeta a gefe an gama yayin ta.

Wani namijin in yaso aure kuma yarasa wani laifi zai mannawa uwargida in aka dameshi da tamabaya wani sai yace ai bata iya tarban baki ba ne saboda a tunanin sa yana ganin kamar ita wacce yake kokarin aurowar tafi kowa hankali ta iya komai dari bisa dari bai san cewa hangen dala yake yi ba.

Wani namijin kuwa sababbin halayensa basa chanzawa sai ya auro ta ya kawo cikin gida daga nan ne labari zai chanza salo in ya hadu da itama amaryar ‘yar garice sai su hada kai da mijin su muzgunawa uwargida, misali akwai gidan da za kaga daga ranar da amarya ta zo to fa baban maganar wanda miji zai saurara akwai gidan da naga amarya ta yi wa uwargida sharrin cewa tana bin malamai saboda tana gane ganecin tana bacci irin wannan sharrin kamata ya yi ace mijin ya yi hukunci mai karfi amma abin mamaki sai ya goyi bayan amarya a kan cewa ya yarda uwargida na bin boka.

Mai yasa, duk tsawon shekarun da suka yi da uwargidan bai fada mata tana bin malamai ba saida ya karo aure, abubuwa makamantan haka suna faruwa a gidajen aure daban daban a duk sanda miji ya dau kdamaran karo aure.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?
Taskira

Me Ya Sa Wasu Maza Ke Gudun Auren Mata ‘Yan Boko Masu Kwarewa Da Wayewa?

August 31, 2025
Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa
Taskira

Yadda Wasu Iyaye Ke Hana ‘Ya’yansu Auren Matan Da Suka Girme Su Da Zawarawa

August 17, 2025
Maza
Taskira

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
Next Post
An Yi Atisayen Karshe Na Dukkan Fannoni Don Share Fagen Karbar Kumbon Shenzhou-14

An Yi Atisayen Karshe Na Dukkan Fannoni Don Share Fagen Karbar Kumbon Shenzhou-14

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version