• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ke Neman Bata Mana Suna Kan Rikicin Shugabancin APGA – INEC

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa surutan da wasu ke yi kan cewa ta ƙi bin umarnin kotu dangane da rikicin shugabancin jam’iyyar APGA wani yunƙuri ne na ɓata mata suna.

 

Babban Kwamishina kuma shugaban Kwamitin Wayar da Kan Masu Zaɓe na hukumar, Lauya Festus Okoye, ya faɗi a wata sanarwa ga manema labarai cewa hukumar ta lura da yadda wata ƙungiya da ba a gane kan ta ba ta ke yamaɗiɗi kan al’amarin, ta na rarraba fastoci da yin surutai inda ta ke zargin hukumar da ƙin bin umarnin Kotun Ƙoli da ya ce wai wani mai suna Cif Edozie Njoku ne “Shugaban APGA na Ƙasa na gaskiya”.

  • Shugaban NIS Ya Nemi Birtaniya Ta Rika Mutunta Bakin Hauren Nijeriya

Hukumar ta ce ana yaɗa waɗannan fastocin da surutan ne don kawai a yi wa INEC sharri da nufin a yaudari waɗanda ba su san gaskiyar abin da ke faruwa ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Okoye ya ce: “Mu na so mu bayyana cewa waɗannan al’amurra fa sun shafi faɗin gaskiya ne tare da bin doka da oda ba wai kwakwazo da neman tada zaune tsaye ba.

 

“A lura da cewa ƙarar da aka kai kotu ta samo asali ne daga Babbar Kotun Jihar Jigawa, wadda wani mai suna Alhaji Rabi’u Garba Aliyu ya kai a kan Cif Jude Okeke da wasu mutum uku. Cif Edozie Njoku ba ya cikin waɗanda ake ƙara.

 

“Ɗaya daga cikin buƙatun da aka nema a wajen kotu shi ne ‘A bayyana cewa shugabannin jam’iyyar All Progressives Grand Alliance na ƙasa, ciki har da mai ƙarar, waɗanda aka zaɓo su a babban taron ta na ƙasa da aka yi a Owerri, Jihar Imo, a ranar 31 ga Mayu 2019, su ci gaba da riƙe muƙaman su tare da yin ayyukan su har tsawon wa’adin shekara huɗu da za a lissafa daga ranar 31 ga Mayu 2021’.

 

“A ranar 30 ga Yuni 2021, Babbar Kotun Jihar Jigawa, a ƙara mai Lamba: JDU/022/2021 ta yanke hukunci inda ta ba wannan Alhaji Rabi’u Garba Aliyu nasara. Da aka ɗaukaka ƙarar, sai Kotun Ɗaukaka Ƙara ta bayyana cewa ƙarar da aka kai ba a bi dokar yin shari’a ba. Don haka, dukkan shari’ar da aka yi a Babbar Kotun Jihar Jigawa a ƙara mai Lamba JDU/022/2021, wadda Musa Ubale J ya yanke a ranar 30 ga Yuni 2021 da hukuncin da aka yanke mata duk an hamɓarar da su.”

 

Kotun Ƙoli, a hukuncin da ta yanke a ranar 14 ga Oktoba 2021, ta tabbatar da hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta zartar.

 

“Sai dai kuma, a ranar 27 ga Janairu 2023, Cif Edozie Njoku, wanda bai taɓa zama cikin dukkan waɗancan shari’u da aka yi a kotuna daban-daban ba, ya je Kotun Ƙoli ta Nijeriya a matsayin wani wanda ke da ta cewa, ya shigar da buƙatar kotun ta yi gyara a ‘kuskuren rubutu da tuntuɓen alƙalami’ a ainihin babban hukuncin da Kotun Ƙolin ta zartar. An amince masa da hakan, kuma gyaran da aka yi bai shafi gundarin ƙarar da kuma hukuncin da Kotun Ƙolin ta riga ta yanke ba.”

 

A cewar Okoye, Hukumar Zaɓe hukuma ce mai bin doka da oda kuma za ta ci gaba da bin duk wata doka ko wani hukunci ko umarni da kotuna daban-daban su ka bayar a duk faɗin Nijeriya.

 

Ya ce, “Ba a ƙin bin umarnin kotunan idan sun ba da umarni ko su ka yanke hukunci ko wata shawara. Kuma su na da ƙarfin hukunta duk wanda ya yi masu tsaurin ido ya ƙi bin umarnin su da hukuncin su a tsarin da su ke da shi. Wannan shi ne abin da duk wani ɗan ƙasa ko wata ƙungiya da ya ke bin doka ya sani, maimakon ya koma ya na neman cin zarafi ko tursasawa ta hanyar wasu ƙungiyoyi marasa alƙibla don kawai a ɓata sunan hukumar da jami’an ta.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Samfurin Tianzhou-6

Next Post

Sin: Kasashen G7 Suna Wakiltar Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa

Related

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
Labarai

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

12 minutes ago
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye
Manyan Labarai

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

2 hours ago
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

4 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a
Manyan Labarai

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

5 hours ago
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

14 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

15 hours ago
Next Post
Sin: Kasashen G7 Suna Wakiltar Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa

Sin: Kasashen G7 Suna Wakiltar Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja

September 9, 2025
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

September 9, 2025
Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

Nan Gaba TIinubu A Wajen Opay Da Moniepoint Zai Nemi Rancen Kuɗi – Dino Melaye

September 9, 2025
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙara Kan Zargin Ƴansanda Da Cin Zarafinsa A Kaduna

September 9, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

Gini Ya Rushe A Jigawa, Mutum 1 Ya Rasu, 7 Sun Jikkata

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.