ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Ke Neman Bata Mana Suna Kan Rikicin Shugabancin APGA – INEC

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa surutan da wasu ke yi kan cewa ta ƙi bin umarnin kotu dangane da rikicin shugabancin jam’iyyar APGA wani yunƙuri ne na ɓata mata suna.

 

Babban Kwamishina kuma shugaban Kwamitin Wayar da Kan Masu Zaɓe na hukumar, Lauya Festus Okoye, ya faɗi a wata sanarwa ga manema labarai cewa hukumar ta lura da yadda wata ƙungiya da ba a gane kan ta ba ta ke yamaɗiɗi kan al’amarin, ta na rarraba fastoci da yin surutai inda ta ke zargin hukumar da ƙin bin umarnin Kotun Ƙoli da ya ce wai wani mai suna Cif Edozie Njoku ne “Shugaban APGA na Ƙasa na gaskiya”.

ADVERTISEMENT
  • Shugaban NIS Ya Nemi Birtaniya Ta Rika Mutunta Bakin Hauren Nijeriya

Hukumar ta ce ana yaɗa waɗannan fastocin da surutan ne don kawai a yi wa INEC sharri da nufin a yaudari waɗanda ba su san gaskiyar abin da ke faruwa ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Okoye ya ce: “Mu na so mu bayyana cewa waɗannan al’amurra fa sun shafi faɗin gaskiya ne tare da bin doka da oda ba wai kwakwazo da neman tada zaune tsaye ba.

 

“A lura da cewa ƙarar da aka kai kotu ta samo asali ne daga Babbar Kotun Jihar Jigawa, wadda wani mai suna Alhaji Rabi’u Garba Aliyu ya kai a kan Cif Jude Okeke da wasu mutum uku. Cif Edozie Njoku ba ya cikin waɗanda ake ƙara.

 

“Ɗaya daga cikin buƙatun da aka nema a wajen kotu shi ne ‘A bayyana cewa shugabannin jam’iyyar All Progressives Grand Alliance na ƙasa, ciki har da mai ƙarar, waɗanda aka zaɓo su a babban taron ta na ƙasa da aka yi a Owerri, Jihar Imo, a ranar 31 ga Mayu 2019, su ci gaba da riƙe muƙaman su tare da yin ayyukan su har tsawon wa’adin shekara huɗu da za a lissafa daga ranar 31 ga Mayu 2021’.

 

“A ranar 30 ga Yuni 2021, Babbar Kotun Jihar Jigawa, a ƙara mai Lamba: JDU/022/2021 ta yanke hukunci inda ta ba wannan Alhaji Rabi’u Garba Aliyu nasara. Da aka ɗaukaka ƙarar, sai Kotun Ɗaukaka Ƙara ta bayyana cewa ƙarar da aka kai ba a bi dokar yin shari’a ba. Don haka, dukkan shari’ar da aka yi a Babbar Kotun Jihar Jigawa a ƙara mai Lamba JDU/022/2021, wadda Musa Ubale J ya yanke a ranar 30 ga Yuni 2021 da hukuncin da aka yanke mata duk an hamɓarar da su.”

 

Kotun Ƙoli, a hukuncin da ta yanke a ranar 14 ga Oktoba 2021, ta tabbatar da hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta zartar.

 

“Sai dai kuma, a ranar 27 ga Janairu 2023, Cif Edozie Njoku, wanda bai taɓa zama cikin dukkan waɗancan shari’u da aka yi a kotuna daban-daban ba, ya je Kotun Ƙoli ta Nijeriya a matsayin wani wanda ke da ta cewa, ya shigar da buƙatar kotun ta yi gyara a ‘kuskuren rubutu da tuntuɓen alƙalami’ a ainihin babban hukuncin da Kotun Ƙolin ta zartar. An amince masa da hakan, kuma gyaran da aka yi bai shafi gundarin ƙarar da kuma hukuncin da Kotun Ƙolin ta riga ta yanke ba.”

 

A cewar Okoye, Hukumar Zaɓe hukuma ce mai bin doka da oda kuma za ta ci gaba da bin duk wata doka ko wani hukunci ko umarni da kotuna daban-daban su ka bayar a duk faɗin Nijeriya.

 

Ya ce, “Ba a ƙin bin umarnin kotunan idan sun ba da umarni ko su ka yanke hukunci ko wata shawara. Kuma su na da ƙarfin hukunta duk wanda ya yi masu tsaurin ido ya ƙi bin umarnin su da hukuncin su a tsarin da su ke da shi. Wannan shi ne abin da duk wani ɗan ƙasa ko wata ƙungiya da ya ke bin doka ya sani, maimakon ya koma ya na neman cin zarafi ko tursasawa ta hanyar wasu ƙungiyoyi marasa alƙibla don kawai a ɓata sunan hukumar da jami’an ta.”

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin: Kasashen G7 Suna Wakiltar Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa

Sin: Kasashen G7 Suna Wakiltar Sabawa Ka’idojin Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.