• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)

by Bilkisu Tijjani
10 months ago
in Labarai
0
Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aisha Yesufu

Aisha Yesufu ta kasance mai kokarin kare hakkin dan’Adam ce, sannan kuma tana kokari a fannin siyasa, kuma ta kasance ‘yar kasuwa ce, maia iyakar kokari akan ta ga ta yi adalci ko an yi wa mutum adalci, ta kasance tana cikin kungiyar nan da aka fi sani da ( Bring BackOurGirls,) Aannan ta ja hankalin mutanen duniya bayan dauke ‘yan matan Chibok sama da 200 da kungiyar ta’addanci ta Boko Haram ta yi a ranar 14 ga watan Afrilu 2014.

Aisha kuma wata jigo ce a masu zanga-zangar EndSaRS, ta nuna rashin amincewa da zaluncin ‘yansanda a Najeriya. Ta samu karbuwa sosai da ta yi haka.

  • What Women Hard anodized cookware Need within a Marriage
  • Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Kazalika tana daya daga cikin mata dari 100 na BBC a shekara ta 2020, kuma an saka su cikin manya dari 100 wadanda suka shahara a New African Magazine a wannan shekarar. A shekara ta 2023 Reputation Poll International ta amince da ita da a matsayin daya daga cikin ‘yan Afirika 100 da suka yi fice, sannan ta kasance cikin jerin mutane 50 da suka yi fice a ranar mata ta duniya a shekara 2023. Shawarar da Aisha ta bayar na ci gaba da da zaburar da mutane da yawa a fagen fafutukar kare hakkin dan‘Adam da adalci na zamantakewa.

Halima Buba

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Halima Buba ‘yar kasuwa kuma ma’aikaciyar banki ce tana matsayin Manajan Darakta kuma shugaba a Bankin Sun Trust bank Plc, ta samu wannan matsayin a Janairu 2021. Kafin wannan mukamin, ta kasance Mataimakiyar Manaja a Ecobank Nigeria.

Ta yi kyakkyawan aiki da ya shafi manyan cibiyoyin hada-hadar kudi ciki har da ‘ Allstates Trust Bank’ , Zenith Bank, Inland Bank Plc, Oceanic Bank Plc, da Ecobank Nigeria Limited. Halima Buba tana cikin wadanda suka samu kwarewa a fannin aikin banki. Bayan aikinta na banki, ta kasance mai ba da shawara ga matasa ga mata kuma ta himmatu wajen ci gaba da ba da ilimin a Nijeriya.

Lami Tumaka

Lami Tumaka ta kasance kwararriyar ko kuma wadda ta iya hulda da jama’a, mai gudanarwa, kuma mai magana da jama’a ce tafi shekaru 30 da kwarewa. Kwarewarta a fannin hulda da jama’a ta bayyana a lokacin da take rike da mukamin manajan hulda da jama’a na kamfanin Peugeot Automobile Nigeria (PAN) Limited, inda ta taka rawar gani wajen daukaka martabar kamfanin.

Kwazon da Tumaka ta nuna daga baya ya kai ta hukumar kula da harkokin jiragen ruwa ta kasa (wanda a yanzu ake kira NIMASA), inda ta yi aiki na tsawon shekaru 22, daga karshe ta kai matsayin Darakta kafin ta yi ritaya ta yi shuhura a sana’arta, ta sami lambobin yabo da yawa, ciki har da watsa labarai ta maritime na shekarar.

Iman Sulaiman Ibrahim

Imaan Sulaiman-Ibrahim fitacciyar ‘yar siyasa ce kuma ‘yar kasuwa mace wacce ta shahara wajen bayar da gudunmawar da ta bayar wajen yi wa gwamnati hidima da gudanar da mulki. Da farko ta rike mukamin Darakta a hukumar hana fataucin bil’ Adama ta kasa (NAPTIP) daga ranar 1 ga Disamba, 2020, zuwa ranar 27 ga Mayu, 2021, daga nan kuma shugaba Muhammadu Buhari ya ba ta mukamin kwamishina ta tarayya ga ‘yan gudun hijira, Baki, da mutunen cikin gida.

Imaan ta kasance da ita aka hada gwiwa kuma shugabar BumbleeBee Cibic Initiatibe, wadda aka fi sani da The Beehibe Initiatibe, wani dandali da aka sadaukar don ciyarwa da horar da mata masu ra’ayin siyasa da fahimtar da jama’a. Ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara ta musamman kan dabarun sadarwa ga Karamin Ministan Ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba, sannan Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya A. A. Sule, a Satumba 2019.

A watan Yulin 2023, Imaan ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko a harkokin ‘yan sanda, wadda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada. Sannan tana nuna kwarewarta ga hidimar jama’a Sana’ar ta na da karfafawa mata da hada kan jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Matan ArewaArewaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Muka Sanya Tinubu Ya Soke Kwangilar Aikin Hanyar Kankara Zuwa Katsina inji Ibrahim Masari 

Next Post

An Kama Wani Matashi A Jigawa Saboda Ƙona Kakarsa

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

3 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

7 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

8 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

9 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

11 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

14 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Matashi A Jigawa Saboda Ƙona Kakarsa

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.