• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Matan Arewa Da Suka Yi Fice (2)

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
Arewa

Aisha Yesufu

Aisha Yesufu ta kasance mai kokarin kare hakkin dan’Adam ce, sannan kuma tana kokari a fannin siyasa, kuma ta kasance ‘yar kasuwa ce, maia iyakar kokari akan ta ga ta yi adalci ko an yi wa mutum adalci, ta kasance tana cikin kungiyar nan da aka fi sani da ( Bring BackOurGirls,) Aannan ta ja hankalin mutanen duniya bayan dauke ‘yan matan Chibok sama da 200 da kungiyar ta’addanci ta Boko Haram ta yi a ranar 14 ga watan Afrilu 2014.

Aisha kuma wata jigo ce a masu zanga-zangar EndSaRS, ta nuna rashin amincewa da zaluncin ‘yansanda a Najeriya. Ta samu karbuwa sosai da ta yi haka.

  • What Women Hard anodized cookware Need within a Marriage
  • Sin Za Ta Samar Da Karin Matakai Daban Daban Na Tallafawa Tattalin Arziki

Kazalika tana daya daga cikin mata dari 100 na BBC a shekara ta 2020, kuma an saka su cikin manya dari 100 wadanda suka shahara a New African Magazine a wannan shekarar. A shekara ta 2023 Reputation Poll International ta amince da ita da a matsayin daya daga cikin ‘yan Afirika 100 da suka yi fice, sannan ta kasance cikin jerin mutane 50 da suka yi fice a ranar mata ta duniya a shekara 2023. Shawarar da Aisha ta bayar na ci gaba da da zaburar da mutane da yawa a fagen fafutukar kare hakkin dan‘Adam da adalci na zamantakewa.

Halima Buba

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Halima Buba ‘yar kasuwa kuma ma’aikaciyar banki ce tana matsayin Manajan Darakta kuma shugaba a Bankin Sun Trust bank Plc, ta samu wannan matsayin a Janairu 2021. Kafin wannan mukamin, ta kasance Mataimakiyar Manaja a Ecobank Nigeria.

Ta yi kyakkyawan aiki da ya shafi manyan cibiyoyin hada-hadar kudi ciki har da ‘ Allstates Trust Bank’ , Zenith Bank, Inland Bank Plc, Oceanic Bank Plc, da Ecobank Nigeria Limited. Halima Buba tana cikin wadanda suka samu kwarewa a fannin aikin banki. Bayan aikinta na banki, ta kasance mai ba da shawara ga matasa ga mata kuma ta himmatu wajen ci gaba da ba da ilimin a Nijeriya.

Lami Tumaka

Lami Tumaka ta kasance kwararriyar ko kuma wadda ta iya hulda da jama’a, mai gudanarwa, kuma mai magana da jama’a ce tafi shekaru 30 da kwarewa. Kwarewarta a fannin hulda da jama’a ta bayyana a lokacin da take rike da mukamin manajan hulda da jama’a na kamfanin Peugeot Automobile Nigeria (PAN) Limited, inda ta taka rawar gani wajen daukaka martabar kamfanin.

Kwazon da Tumaka ta nuna daga baya ya kai ta hukumar kula da harkokin jiragen ruwa ta kasa (wanda a yanzu ake kira NIMASA), inda ta yi aiki na tsawon shekaru 22, daga karshe ta kai matsayin Darakta kafin ta yi ritaya ta yi shuhura a sana’arta, ta sami lambobin yabo da yawa, ciki har da watsa labarai ta maritime na shekarar.

Iman Sulaiman Ibrahim

Imaan Sulaiman-Ibrahim fitacciyar ‘yar siyasa ce kuma ‘yar kasuwa mace wacce ta shahara wajen bayar da gudunmawar da ta bayar wajen yi wa gwamnati hidima da gudanar da mulki. Da farko ta rike mukamin Darakta a hukumar hana fataucin bil’ Adama ta kasa (NAPTIP) daga ranar 1 ga Disamba, 2020, zuwa ranar 27 ga Mayu, 2021, daga nan kuma shugaba Muhammadu Buhari ya ba ta mukamin kwamishina ta tarayya ga ‘yan gudun hijira, Baki, da mutunen cikin gida.

Imaan ta kasance da ita aka hada gwiwa kuma shugabar BumbleeBee Cibic Initiatibe, wadda aka fi sani da The Beehibe Initiatibe, wani dandali da aka sadaukar don ciyarwa da horar da mata masu ra’ayin siyasa da fahimtar da jama’a. Ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara ta musamman kan dabarun sadarwa ga Karamin Ministan Ilimi, Chukwuemeka Nwajiuba, sannan Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya A. A. Sule, a Satumba 2019.

A watan Yulin 2023, Imaan ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko a harkokin ‘yan sanda, wadda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada. Sannan tana nuna kwarewarta ga hidimar jama’a Sana’ar ta na da karfafawa mata da hada kan jama’a.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
Labarai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Matashi A Jigawa Saboda Ƙona Kakarsa

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.