• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wasu Shugabannin Afirka Sun Taya Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin Murnar Cika Shekaru 73 Da Kafuwa

byCMG Hausa
3 years ago
Afirka

A baya-bayan nan, shugabannin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa da dama ne, suka bugu waya ko aiko da wasiku ga Xi Jinping, babban sakataren kwamitin kolin JKS, kuma shugaban jamhuriyar jama’ar kasar Sin, don taya murnar cika shekaru 73 da kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, tare da fatan samun nasarar gudanar da babban taron wakilan JKS karo 20 dake tafe.

A sakonsa, shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari, ya yi fatan babban taron wakilan JKS karo na 20, wanda ke da ma’ana a tarihi, zai gudana cikin nasara.

  • An Kammala Zaben Wakilan Da Za Su Halarci Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

Ya kuma bayyana cewa, yana fatan taron zai fito da wani tsari na ci gaban kasar Sin a nan gaba. Ya kara da cewa, Najeriya na son karfafa cudanya da hadin gwiwa da kasar Sin, da ciyar da dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi.

Shi ma shugaban kasar Ghana, Nana Addo Dankwa Akufo-Addo, ya bayyana cewa, kasar Sin kasa ce mai da’awar tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya, da cudanyar bangarori daban-daban, da tabbatar da adalci da daidaito a duniya.

Ya kara da cewa, kasar Sin ta kuduri aniyar tallafawa ci gaban kasashen Afitrka baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Shugaba Akufo-Addo, ya bayyana cewa, kasarsa na fatan sassan biyu, za su inganta hadin gwiwa a tsakaninsu da hadin gwiwar bangarori daban-daban, da karfafa dankon zumunci a tsakanin al’ummominsu, da gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga daukacin bil-Adama.

A madadin gwamnatin da jama’ar kasar Afirka ta Kudu kuwa shugaban kasar Cyril Ramaphosa, ya mika gaisuwa da taya murna ga shugaba Xi da gwamnati da jama’ar kasar Sin, yana mai jaddada cewa, kasarsa a shirye take ta kara karfafa zumunci da abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin ta da kasar Sin. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
PDP Ta Sake Kwace Kujerar Shugaban Karamar Hukuma Daga Hannun APC A Abuja

PDP Ta Sake Kwace Kujerar Shugaban Karamar Hukuma Daga Hannun APC A Abuja

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version