• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai suna ‘Democracy Defenders Forum’, ta yi barazanar maka Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), reshen Jihar Kebbi a gaban kotu kan gangamin goyon bayan wani dan takarar gwamna a jihar.

Shugaban kungiyar Almustapha Habib-Yauri ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani
  • ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya

Ya ce: “Majalisar ta lura da takaicin takardar da ake yadawa da ake zargin ta fito ne daga kungiyar kwadago, reshen Jihar Kebbi, inda ta gayyaci kungiyoyin siyasa da daidaikun mutane zuwa wani gangami a ranar Talata, 25 ga Oktoba, 2022.

“Taron na nuna goyon baya ne ga Nasiru Idris, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zabe mai zuwa a jihar.”

Habib-Yauri ya ce saboda haka kungiyar ta yi Allah wadai da irin wannan mataki gaba daya, sanin cewa bai dace da dokokin da suka kafa kungiyar ba.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

“Ba mu ci karo da dokokin Nijeriya masu tsayuwa da suka ba da damar ’yancin yin tarayya da jama’a, ciki har da ‘yancin ma’aikata dangane da matsayinsu na siyasa amma ba wai goyon bayan shugabanni na ja da kungiyar a matsayinta na jam’iyya ba.

“Don haka muna kira ga shugabannin kungiyar NLC a jihar da su tabbatar da irin wannan gayyata da ake yadawa tare da yin bayani karara kan hannu ko akasin haka cikin kankanin lokaci,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da cewa “Idan har kungiyar kwadago ta NLC ta amince da sa hannunta kuma ta ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri, za a bar dandalin ba tare da wani zabin da ya wuce maka kungiyar NLC a kotun sauraren kararrakin ma’aikata.

“Kamar yadda muke la’akari ba wai kawai yunkurin da bai dace ba ne amma yunkurin lalata martabar kungiyar kwadago ta Nijeriya da sauran kungiyoyin da ke da alaka da su zai yi, inji shi.”

Da aka tuntubi shugaban NLC reshen Jihar Kebbi, Umar Alhassan-Halidu ya ce: “ Kungiyar za ta gudanar da taron majalisar koli ta kasa a Jihar kebbi a ranar Talata, 24 ga Oktoba.

“Washegari da safe za mu yi tattaki (taron gangami) zuwa filin wasa na Haliru Audu, Nasiru Idris Kauran Gwandu na cikinmu, shi ne mataimakin shugaban NLC na kasa, dole ne mu nuna masa hadin kai da goyon bayan takararsa.

“Idan za a tuna lokacin da Adams Oshomole ya tsaya takara haka aka yi masa a matsayinsa na tsohon shugaban NLC, babu wani sabon abu, a matsayinmu na ma’aikata mu ma muna da jam’iyyarmu, mun yi rajistar Labour Party (LP) don kawai ma’aikatan Nijeriya su samu jam’iyyarsu kuma mun dauki nauyin jam’iyyar, in ji shi.

“A matsayinmu na ma’aikata, ba za mu iya yin zaman banza ba, dole ne mu shiga harkokin siyasa domin mu ma ‘yan Nijeriya ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GangamiJihar KebbiKotuKungiyaNlcSiyasaTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kogi Ta Maka Dangote A Kotu Kan Takaddamar Kamfanin Simintin Obajana

Next Post

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

11 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

17 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

22 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 day ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

1 day ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

1 day ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.