ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kungiyar Kwadago

Wata kungiya mai suna ‘Democracy Defenders Forum’, ta yi barazanar maka Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC), reshen Jihar Kebbi a gaban kotu kan gangamin goyon bayan wani dan takarar gwamna a jihar.

Shugaban kungiyar Almustapha Habib-Yauri ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

  • Zan Daukaka Kara Kan Hukuncin Kotu Da Ya Soke Takarata – Aisha Binani
  • ICPC Ta Rufe Makarantu 68 Na Bogi A Nijeriya

Ya ce: “Majalisar ta lura da takaicin takardar da ake yadawa da ake zargin ta fito ne daga kungiyar kwadago, reshen Jihar Kebbi, inda ta gayyaci kungiyoyin siyasa da daidaikun mutane zuwa wani gangami a ranar Talata, 25 ga Oktoba, 2022.

ADVERTISEMENT

“Taron na nuna goyon baya ne ga Nasiru Idris, dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zabe mai zuwa a jihar.”

Habib-Yauri ya ce saboda haka kungiyar ta yi Allah wadai da irin wannan mataki gaba daya, sanin cewa bai dace da dokokin da suka kafa kungiyar ba.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

“Ba mu ci karo da dokokin Nijeriya masu tsayuwa da suka ba da damar ’yancin yin tarayya da jama’a, ciki har da ‘yancin ma’aikata dangane da matsayinsu na siyasa amma ba wai goyon bayan shugabanni na ja da kungiyar a matsayinta na jam’iyya ba.

“Don haka muna kira ga shugabannin kungiyar NLC a jihar da su tabbatar da irin wannan gayyata da ake yadawa tare da yin bayani karara kan hannu ko akasin haka cikin kankanin lokaci,” in ji shi.

Shugaban ya ci gaba da cewa “Idan har kungiyar kwadago ta NLC ta amince da sa hannunta kuma ta ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri, za a bar dandalin ba tare da wani zabin da ya wuce maka kungiyar NLC a kotun sauraren kararrakin ma’aikata.

“Kamar yadda muke la’akari ba wai kawai yunkurin da bai dace ba ne amma yunkurin lalata martabar kungiyar kwadago ta Nijeriya da sauran kungiyoyin da ke da alaka da su zai yi, inji shi.”

Da aka tuntubi shugaban NLC reshen Jihar Kebbi, Umar Alhassan-Halidu ya ce: “ Kungiyar za ta gudanar da taron majalisar koli ta kasa a Jihar kebbi a ranar Talata, 24 ga Oktoba.

“Washegari da safe za mu yi tattaki (taron gangami) zuwa filin wasa na Haliru Audu, Nasiru Idris Kauran Gwandu na cikinmu, shi ne mataimakin shugaban NLC na kasa, dole ne mu nuna masa hadin kai da goyon bayan takararsa.

“Idan za a tuna lokacin da Adams Oshomole ya tsaya takara haka aka yi masa a matsayinsa na tsohon shugaban NLC, babu wani sabon abu, a matsayinmu na ma’aikata mu ma muna da jam’iyyarmu, mun yi rajistar Labour Party (LP) don kawai ma’aikatan Nijeriya su samu jam’iyyarsu kuma mun dauki nauyin jam’iyyar, in ji shi.

“A matsayinmu na ma’aikata, ba za mu iya yin zaman banza ba, dole ne mu shiga harkokin siyasa domin mu ma ‘yan Nijeriya ne.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.