• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo

by Muhammad
2 months ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Wata Motar Tankar Mai Ta Kama Da Wuta Tare Da Kone Wasu Motoci A Ibadan, Jihar Oyo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wuta ta kone wata tankar mai ɗauke da lita 33,000 na fetur, lamarin ya rutsa da wata mota kirar Toyota Prado Jeep da wata mota a unguwar Celica Junction, kan babbar hanyar Ife-Ibadan Expressway, a birnin Ibadan, babban birnin jihar Oyo.

Manajan da ke kula da sashen ayyuka a Hukumar Kashe Gobara ta Jihar, Akinyemi Akinyinka, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an sanar da su da misalin ƙarfe 6:27 na yamma ta wayar salula a ranar Alhamis.

  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas
  • Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Akinyinka ya ce tawagar jami’an kashe gobara ƙarƙashin jagorancin ACFS Adeniyi Adesina sun garzaya wurin lokacin da abin ya faru.

Da suka isa wurin, sun tarar da tankar mai cike da fetur da wata mota na ci da wuta.

Ya ce ma’aikatan kashe gobara sun fara aiki cikin gaggawa ta hanyar amfani da kumfar kashe gobara, kuma sun hana wutar bazuwa zuwa tashar mai ta NNPC da daƙile ɓarnatar da dukiyoyin da ke kusa da wurin da abin ya afku.

Labarai Masu Nasaba

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

Ya ƙara da cewa, an haɗa kai da jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya wajen kashe wutar gaba ɗaya.

Akinyinka ya bayyana cewa gobarar ta samo asali ne daga matsalar birkin tankar yayin tafiya, lamarin da ya sa ta bugi mota kirar Toyota Prado da wata mota kafin ta faɗi a hanya inda nan-take ta wuta.

“Ba a samu asarar rai ba, amma tankar da mota ɗaya sun kone, yayin da Jeep ɗin ta faɗa cikin wani rami a sakamakon bugun da tankar ta yi mata. Hukumar kashe gobara ta ceci tashar mai ta NNPC da sauran kadarorin da ke kusa daga konewa,” cewar shi.

Mai ba da shawara kan ayyukan kashe gobara kuma shugaban kwamitin, Dr Maroof Akinwande, ya shawarci jama’a da su ci gaba da harkokinsu cikin kwanciyar hankali domin an kashe gobarar gaba ɗaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DukiyoyiGobaraOyoTankar Mai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

Next Post

Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Related

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

4 days ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

5 days ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

4 weeks ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Jami’an Tsaro Sun Kama Manyan Shugabannin Ƙungiyar Ansaru 2

1 month ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

2 months ago
Next Post
Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

Oyo

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

September 21, 2025
Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

September 21, 2025
Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

Kin Amincewar Japan Game Da Muggan Laifukan Yakin Da Ta Aikata Ya Dakatar Da Bukatar Sin Ga Hukumar UNESCO

September 20, 2025
An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

An Gabatar Da Fim Mai Taken Shen Zhou 13 A Kasar Birtaniya

September 20, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Martaba Hakkokin Kamfanoni

September 20, 2025
Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

Abin Fashewa Ya Tarwatse A Masana’antar Ƙera Makamai Ta Sojojin Nijeriya A Kaduna

September 20, 2025
Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

Shugaban Kasar Iran Ya Yi Tsokaci Kan Shawarar Tsarin Inganta Jagorancin Duniya

September 20, 2025
Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.