• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci taro na 23 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin-kai ta Shanghai ko kuma SCO a takaice, da maraicen yau Talata 4 ga wata a Beijing, inda ya gabatar da muhimmin jawabi.

A jawabin nasa, Xi ya nuna cewa, a halin yanzu duniyar mu tana fuskantar rikice-rikice da yawa, kana, dan Adam na fuskantar kalubalen da ba’a taba ganin irinsa ba.

  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Musaya Da Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

Tambaya a nan ita ce, hadin-gwiwa ko rarrabuwar kawuna, zaman lafiya ko rikice-rikice, zaman tsintsiya madaurinki daya ko zaman fito-na-fito, wane ake bukata? Amsa ta ita ce, fatan al’ummun kasa da kasa game da more rayuwa mai dadi, shi ne babban aikin dake gaban mu, kana kuma, babu wani mutum ko wata kasa, da za ta iya hana ayyukan wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da inganta hadin-gwiwa, da neman cimma moriya tare a duniyar mu.

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa, kasar sa na fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, don aiwatar da shawarar tabbatar da tsaro a duk fadin duniya, da daidaita sabani tsakanin kasa da kasa ta hanyar yin shawarwari, da taimakawa wajen warware matsalolin kasa da kasa da na shiyya-shiyya ta hanyar siyasa.

Kaza lika kasar Sin tana kuma fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, wajen tabbatar da shawarar samar da ci gaban duk duniya, da tsayawa kan kokarin dunkule tattalin arzikin duniya na bai daya, da nuna adawa ga ra’ayin bada kariya, da sanya takunkumi a gefe daya, da ra’ayin nuna wariya da rarrabuwar kawuna, a wani kokari na kara samun nasarori don su amfani al’ummun kowace kasa bisa adalci. Kasar Sin tana maraba da bangarori daban-daban, da su aiwatar da shawarar inganta wayewar kai a duk fadin duniya, da nuna hakuri ga mabambantan al’adu, don kara samun fahimtar juna, da sada zumunta tsakanin jama’ar kasashe daban-daban.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

A bana ne ake cika shekaru 10, tun bayan da kasar Sin ta bullo da shawarar “ziri daya da hanya daya”, inda za ta gudanar da babban dandalin tattaunawa na hadin-gwiwar kasa da kasa bisa shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3. Game da hakan, shugaba Xi ya ce, yana maraba da halartar bangarori daban-daban dandalin, ta yadda shawarar za ta kara samar da alfanu ga jama’ar duk fadin duniya. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsinci Jariri A Raye A Bayan Mahaifiyarsa Awa 24 Bayan Kashe Ta

Next Post

Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

Related

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

56 minutes ago
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

1 hour ago
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

3 hours ago
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

3 hours ago
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

5 hours ago
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

6 hours ago
Next Post
Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.