• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

by CMG Hausa
2 years ago
Xi Jinping

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci taro na 23 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin-kai ta Shanghai ko kuma SCO a takaice, da maraicen yau Talata 4 ga wata a Beijing, inda ya gabatar da muhimmin jawabi.

A jawabin nasa, Xi ya nuna cewa, a halin yanzu duniyar mu tana fuskantar rikice-rikice da yawa, kana, dan Adam na fuskantar kalubalen da ba’a taba ganin irinsa ba.

  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Musaya Da Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

Tambaya a nan ita ce, hadin-gwiwa ko rarrabuwar kawuna, zaman lafiya ko rikice-rikice, zaman tsintsiya madaurinki daya ko zaman fito-na-fito, wane ake bukata? Amsa ta ita ce, fatan al’ummun kasa da kasa game da more rayuwa mai dadi, shi ne babban aikin dake gaban mu, kana kuma, babu wani mutum ko wata kasa, da za ta iya hana ayyukan wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da inganta hadin-gwiwa, da neman cimma moriya tare a duniyar mu.

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa, kasar sa na fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, don aiwatar da shawarar tabbatar da tsaro a duk fadin duniya, da daidaita sabani tsakanin kasa da kasa ta hanyar yin shawarwari, da taimakawa wajen warware matsalolin kasa da kasa da na shiyya-shiyya ta hanyar siyasa.

Kaza lika kasar Sin tana kuma fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, wajen tabbatar da shawarar samar da ci gaban duk duniya, da tsayawa kan kokarin dunkule tattalin arzikin duniya na bai daya, da nuna adawa ga ra’ayin bada kariya, da sanya takunkumi a gefe daya, da ra’ayin nuna wariya da rarrabuwar kawuna, a wani kokari na kara samun nasarori don su amfani al’ummun kowace kasa bisa adalci. Kasar Sin tana maraba da bangarori daban-daban, da su aiwatar da shawarar inganta wayewar kai a duk fadin duniya, da nuna hakuri ga mabambantan al’adu, don kara samun fahimtar juna, da sada zumunta tsakanin jama’ar kasashe daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

A bana ne ake cika shekaru 10, tun bayan da kasar Sin ta bullo da shawarar “ziri daya da hanya daya”, inda za ta gudanar da babban dandalin tattaunawa na hadin-gwiwar kasa da kasa bisa shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3. Game da hakan, shugaba Xi ya ce, yana maraba da halartar bangarori daban-daban dandalin, ta yadda shawarar za ta kara samar da alfanu ga jama’ar duk fadin duniya. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
Next Post
Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.