ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping: Ba Za’a Iya Hana Ayyukan Shimfida Zaman Lafiya Da Samar Da Ci Gaba Da Inganta Hadin-Gwiwa Da Cimma Moriya Tare Ba

by CMG Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarci taro na 23 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin-kai ta Shanghai ko kuma SCO a takaice, da maraicen yau Talata 4 ga wata a Beijing, inda ya gabatar da muhimmin jawabi.

A jawabin nasa, Xi ya nuna cewa, a halin yanzu duniyar mu tana fuskantar rikice-rikice da yawa, kana, dan Adam na fuskantar kalubalen da ba’a taba ganin irinsa ba.

  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Musaya Da Koyi Da Juna Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai

Tambaya a nan ita ce, hadin-gwiwa ko rarrabuwar kawuna, zaman lafiya ko rikice-rikice, zaman tsintsiya madaurinki daya ko zaman fito-na-fito, wane ake bukata? Amsa ta ita ce, fatan al’ummun kasa da kasa game da more rayuwa mai dadi, shi ne babban aikin dake gaban mu, kana kuma, babu wani mutum ko wata kasa, da za ta iya hana ayyukan wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da inganta hadin-gwiwa, da neman cimma moriya tare a duniyar mu.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa, kasar sa na fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, don aiwatar da shawarar tabbatar da tsaro a duk fadin duniya, da daidaita sabani tsakanin kasa da kasa ta hanyar yin shawarwari, da taimakawa wajen warware matsalolin kasa da kasa da na shiyya-shiyya ta hanyar siyasa.

Kaza lika kasar Sin tana kuma fatan yin kokari tare da bangarori daban-daban, wajen tabbatar da shawarar samar da ci gaban duk duniya, da tsayawa kan kokarin dunkule tattalin arzikin duniya na bai daya, da nuna adawa ga ra’ayin bada kariya, da sanya takunkumi a gefe daya, da ra’ayin nuna wariya da rarrabuwar kawuna, a wani kokari na kara samun nasarori don su amfani al’ummun kowace kasa bisa adalci. Kasar Sin tana maraba da bangarori daban-daban, da su aiwatar da shawarar inganta wayewar kai a duk fadin duniya, da nuna hakuri ga mabambantan al’adu, don kara samun fahimtar juna, da sada zumunta tsakanin jama’ar kasashe daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

A bana ne ake cika shekaru 10, tun bayan da kasar Sin ta bullo da shawarar “ziri daya da hanya daya”, inda za ta gudanar da babban dandalin tattaunawa na hadin-gwiwar kasa da kasa bisa shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3. Game da hakan, shugaba Xi ya ce, yana maraba da halartar bangarori daban-daban dandalin, ta yadda shawarar za ta kara samar da alfanu ga jama’ar duk fadin duniya. (Murtala Zhang)

Xi Jinping
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

Hajji 2023: Rukunin Farko Na Alhazan Nijeriya Sun Baro Saudiyya Zuwa Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.