Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da muhimmin umarni, biyo bayan rugujewar wata mahakar ma’adanin kwal a Mongoliya ta gida, inda ya bukaci da a yi duk mai yiwuwa wajen ganowa tare da ceto wadanda suka bace, da kula da wadanda suka jikkata, da kuma kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
A yau ne da misalin karfe 1 na rana, aka samu wani gagarumin rugujewar wata mahakar ma’adanin kwal a yankin Alxa dake Mongoliya ta gida, kuma ya zuwa yanzu, hadarin ya yi sanadiyar mutuwar mutane 2, tare da jikkata mutane 6, yayin da mutane 53 suka bace. (Ibrahim Yaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp