• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 15 ga watan Nuwamba, bisa agogon wurin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Amurka, Joe Biden, a wani wurin da ake kira Filoli a birnin San Francisco na kasar Amurka.

Xi ya ce, yanzu shekara daya ta wuce, tun bayan ganawarsa da Biden a tsibirin Bali. Kuma a shekara daya da ta gabata, abubuwa da dama sun wakana. Duniya ta samo mafita daga yaduwar cutar mashako ta COVID-19, amma har yanzu annobar na haifar da babban tasiri. Kana, tattalin arzikin duniya ya fara murmurewa, amma ba shi da karfi sosai, al’amarin da ya kawo tsaiko ga tsarin sana’o’i, da tsarin samar da kayayyaki, kuma ra’ayin bada kariya ga harkokin cinikayya na kara tsananta. A matsayinta na alakar bangarori biyu mafi muhimmanci a duniya, kamata ya yi a yi la’akari, gami da tsara shirin raya dangantakar Sin da Amurka daidai bisa yanayin da ake ciki yanzu, wato gaggauta samun sauye-sauye a duniya, ta yadda za’a samar da alfanu ga al’ummomin kasashen biyu, da zama abun misali ga ci gaban harkokin dan Adam.

  • Sinawa Masana Kimiyya Sama Da 1,200 Ne Suka Shiga Cikin Jerin Masu Bincike Da Aka Fi Amfani Da Ayyukansu A Duniya
  • Shugaba Xi Ya Isa Birnin San Francisco Don Ganawa Da Takwaransa Na Amurka Da Halartar Taron Shugabannin Mambobin Kungiyar APEC

Shugaba Xi ya kara da cewa, cikin sama da shekaru 50 da suka gabata, dangantakar Sin da Amurka ta sha fuskantar matsaloli iri-iri. Duk da cewa akwai sabani, amma tana samun ci gaba. Ba zai yiwu irin wadannan manyan kasashe biyu su zamo ba sa mu’amala da juna ba. Kana, duk wani yunkuri na wani bangare na sauya dayan bangaren, ba zai ci nasara ba, kuma babu wani bangaren da zai iya jure sakamakon rikicinsu.

Ya ce, har yanzu ina da imanin cewa, takara tsakanin manyan kasashe masu karfin fada a ji ba ita ce taken wannan zamani ba, kuma ba za ta warware matsalolin Sin da na Amurka da na duniya baki daya ba. Wannan duniya na da fadin da zai wadatar da Sin da Amurka, kuma nasarorin mu damammaki ne gare mu baki daya. Banbancin tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa, da turbar ci gaban Sin da Amurka al’amura ne na zahiri. Ko shakka ba bu, muddin bangarorin biyu sun rungumi akidun mutunta juna, da zaman jituwa, da hadin gwiwar cimma moriya tare, za su iya shawo kan daukacin banbance banbance, tare da lalubo hanya mafi dacewa ta zaman jituwa tsakanin wadannan kasashe biyu masu karfi a duniya. Ina da yakinin cewa, alakar Sin da Amurka na da kyakkyawar makoma.

Ya ce, ni da shugaban kasa, muna jagorantar alakar Sin da Amurka, muna dauke da nauyin al’ummun mu, da duniya, da tarihi. A yau ina fatan zurfafa musayar ra’ayoyi tare da shugaban kasa, kan batutuwan da suka jibanci alakar Sin da Amurka, da ma manyan batutuwan da suka shafi wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya, tare da cimma sabon daidaito. (Murtala Zhang, Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaJoe BidenXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Jaddada Bukatar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu

Next Post

Ofishin Jakadancin Saudiyya A Nijeriya Ya Yi Bayani Kan Soke Bizar Fasinjojin Nijeriya

Related

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

1 minute ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

1 hour ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

2 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

3 hours ago
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan
Daga Birnin Sin

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

4 hours ago
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

5 hours ago
Next Post
Saudiyya

Ofishin Jakadancin Saudiyya A Nijeriya Ya Yi Bayani Kan Soke Bizar Fasinjojin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.