ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

by CGTN Hausa
3 years ago
Xi

A ranar 15 ga watan Nuwamba, bisa agogon wurin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Amurka, Joe Biden, a wani wurin da ake kira Filoli a birnin San Francisco na kasar Amurka.

Xi ya ce, yanzu shekara daya ta wuce, tun bayan ganawarsa da Biden a tsibirin Bali. Kuma a shekara daya da ta gabata, abubuwa da dama sun wakana. Duniya ta samo mafita daga yaduwar cutar mashako ta COVID-19, amma har yanzu annobar na haifar da babban tasiri. Kana, tattalin arzikin duniya ya fara murmurewa, amma ba shi da karfi sosai, al’amarin da ya kawo tsaiko ga tsarin sana’o’i, da tsarin samar da kayayyaki, kuma ra’ayin bada kariya ga harkokin cinikayya na kara tsananta. A matsayinta na alakar bangarori biyu mafi muhimmanci a duniya, kamata ya yi a yi la’akari, gami da tsara shirin raya dangantakar Sin da Amurka daidai bisa yanayin da ake ciki yanzu, wato gaggauta samun sauye-sauye a duniya, ta yadda za’a samar da alfanu ga al’ummomin kasashen biyu, da zama abun misali ga ci gaban harkokin dan Adam.

  • Sinawa Masana Kimiyya Sama Da 1,200 Ne Suka Shiga Cikin Jerin Masu Bincike Da Aka Fi Amfani Da Ayyukansu A Duniya
  • Shugaba Xi Ya Isa Birnin San Francisco Don Ganawa Da Takwaransa Na Amurka Da Halartar Taron Shugabannin Mambobin Kungiyar APEC

Shugaba Xi ya kara da cewa, cikin sama da shekaru 50 da suka gabata, dangantakar Sin da Amurka ta sha fuskantar matsaloli iri-iri. Duk da cewa akwai sabani, amma tana samun ci gaba. Ba zai yiwu irin wadannan manyan kasashe biyu su zamo ba sa mu’amala da juna ba. Kana, duk wani yunkuri na wani bangare na sauya dayan bangaren, ba zai ci nasara ba, kuma babu wani bangaren da zai iya jure sakamakon rikicinsu.

ADVERTISEMENT

Ya ce, har yanzu ina da imanin cewa, takara tsakanin manyan kasashe masu karfin fada a ji ba ita ce taken wannan zamani ba, kuma ba za ta warware matsalolin Sin da na Amurka da na duniya baki daya ba. Wannan duniya na da fadin da zai wadatar da Sin da Amurka, kuma nasarorin mu damammaki ne gare mu baki daya. Banbancin tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa, da turbar ci gaban Sin da Amurka al’amura ne na zahiri. Ko shakka ba bu, muddin bangarorin biyu sun rungumi akidun mutunta juna, da zaman jituwa, da hadin gwiwar cimma moriya tare, za su iya shawo kan daukacin banbance banbance, tare da lalubo hanya mafi dacewa ta zaman jituwa tsakanin wadannan kasashe biyu masu karfi a duniya. Ina da yakinin cewa, alakar Sin da Amurka na da kyakkyawar makoma.

Ya ce, ni da shugaban kasa, muna jagorantar alakar Sin da Amurka, muna dauke da nauyin al’ummun mu, da duniya, da tarihi. A yau ina fatan zurfafa musayar ra’ayoyi tare da shugaban kasa, kan batutuwan da suka jibanci alakar Sin da Amurka, da ma manyan batutuwan da suka shafi wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya, tare da cimma sabon daidaito. (Murtala Zhang, Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

 

Xi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Saudiyya

Ofishin Jakadancin Saudiyya A Nijeriya Ya Yi Bayani Kan Soke Bizar Fasinjojin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.