ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

by CGTN Hausa
3 years ago
Xi

A ranar 15 ga watan Nuwamba, bisa agogon wurin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Amurka, Joe Biden, a wani wurin da ake kira Filoli a birnin San Francisco na kasar Amurka.

Xi ya ce, yanzu shekara daya ta wuce, tun bayan ganawarsa da Biden a tsibirin Bali. Kuma a shekara daya da ta gabata, abubuwa da dama sun wakana. Duniya ta samo mafita daga yaduwar cutar mashako ta COVID-19, amma har yanzu annobar na haifar da babban tasiri. Kana, tattalin arzikin duniya ya fara murmurewa, amma ba shi da karfi sosai, al’amarin da ya kawo tsaiko ga tsarin sana’o’i, da tsarin samar da kayayyaki, kuma ra’ayin bada kariya ga harkokin cinikayya na kara tsananta. A matsayinta na alakar bangarori biyu mafi muhimmanci a duniya, kamata ya yi a yi la’akari, gami da tsara shirin raya dangantakar Sin da Amurka daidai bisa yanayin da ake ciki yanzu, wato gaggauta samun sauye-sauye a duniya, ta yadda za’a samar da alfanu ga al’ummomin kasashen biyu, da zama abun misali ga ci gaban harkokin dan Adam.

  • Sinawa Masana Kimiyya Sama Da 1,200 Ne Suka Shiga Cikin Jerin Masu Bincike Da Aka Fi Amfani Da Ayyukansu A Duniya
  • Shugaba Xi Ya Isa Birnin San Francisco Don Ganawa Da Takwaransa Na Amurka Da Halartar Taron Shugabannin Mambobin Kungiyar APEC

Shugaba Xi ya kara da cewa, cikin sama da shekaru 50 da suka gabata, dangantakar Sin da Amurka ta sha fuskantar matsaloli iri-iri. Duk da cewa akwai sabani, amma tana samun ci gaba. Ba zai yiwu irin wadannan manyan kasashe biyu su zamo ba sa mu’amala da juna ba. Kana, duk wani yunkuri na wani bangare na sauya dayan bangaren, ba zai ci nasara ba, kuma babu wani bangaren da zai iya jure sakamakon rikicinsu.

ADVERTISEMENT

Ya ce, har yanzu ina da imanin cewa, takara tsakanin manyan kasashe masu karfin fada a ji ba ita ce taken wannan zamani ba, kuma ba za ta warware matsalolin Sin da na Amurka da na duniya baki daya ba. Wannan duniya na da fadin da zai wadatar da Sin da Amurka, kuma nasarorin mu damammaki ne gare mu baki daya. Banbancin tarihi, da al’adu, da tsarin zamantakewa, da turbar ci gaban Sin da Amurka al’amura ne na zahiri. Ko shakka ba bu, muddin bangarorin biyu sun rungumi akidun mutunta juna, da zaman jituwa, da hadin gwiwar cimma moriya tare, za su iya shawo kan daukacin banbance banbance, tare da lalubo hanya mafi dacewa ta zaman jituwa tsakanin wadannan kasashe biyu masu karfi a duniya. Ina da yakinin cewa, alakar Sin da Amurka na da kyakkyawar makoma.

Ya ce, ni da shugaban kasa, muna jagorantar alakar Sin da Amurka, muna dauke da nauyin al’ummun mu, da duniya, da tarihi. A yau ina fatan zurfafa musayar ra’ayoyi tare da shugaban kasa, kan batutuwan da suka jibanci alakar Sin da Amurka, da ma manyan batutuwan da suka shafi wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya, tare da cimma sabon daidaito. (Murtala Zhang, Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

 

Xi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Next Post
Saudiyya

Ofishin Jakadancin Saudiyya A Nijeriya Ya Yi Bayani Kan Soke Bizar Fasinjojin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.