• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Benin Da Kuma Aika Sakwanni Ga Takwarorinsa na Zimbabwe Da AFirka Ta Kudu

by CMG Hausa
2 years ago
Xi Jinping

Da yammacin yau Juma’a ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya tattauna da takwaransa na kasar Benin Patrice Talon, wanda ke ziyarar aiki a nan birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka sanar da kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

Xi Jinping ya nuna cewa, Sin na goyon bayan nahiyar Afrika, a fannin zama wani muhimmin bangare na siyasa, da tattalin arziki, da al’adu a duniya, tana kuma mai fatan samar da sabbin damammaki bisa ci gaban da take samu, da kuma hadin kai da kasashen Afirka ciki har da Benin, don tabbatar da ci gaban da aka samu, a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afrika, da ingiza shawarar “ziri daya da hanya daya”, da shawarar raya duniya ta bai daya, da ma ajandar 2063 ta AU, da kuma tabbatar da tsare-tsaren bunkasuwar kasashen Afrika, har ma da goyon bayan kasashen nahiyar wajen samun farfadowar tattalin arziki, da bunkasuwa mai dorewa.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin

A nasa bangare, Patrice Talon cewa ya yi, shugabannin biyu sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwarsu a fannoni daban-daban, ciki har da zurfafa hadin kai wajen tabbatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da samun bunkasuwa, tare da kiyaye muhalli, da kayayyakin aikin gona, da kiwo lafiya da sauransu. Ban da wannan kuma, an gabatar da sanarwar kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu.

Sannan, a Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya takwaransa na kasar Zimbabwe Emmerson Dambudzo Mnangagwa, murnar zarcewa a mukamin shugaban kasa.

A sakon na sa ta wayar tarho, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, Sin da Zimbabwe na da hulda mai kyau. Kaza lika a shekarun baya-bayan nan, kasashen biyu na karfafa fahimtar juna a siyasance, tare da samun sakamako mai armashi a fannin hadin kai, da goyon bayan juna kan muradunsu masu tushe, a karkashin jagorancin shugabannin biyu.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

Xi ya kara da cewa, Sin na dora muhimmanci matuka kan bunkasuwar huldar kasashen biyu, yana kuma mai fatan kara hadin kai da Emmerson Dambudzo Mnangagwa, a fannin ingiza samun sabon ci gaba, ta fuskar huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kiyaye adalci da daidaito na kasa da kasa, da muradun bai daya na kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, a yau Juma’a shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jajantawa takwaransa na kasar Afrika ta kudu Matamela Cyril Ramaphosa, bisa gobara da ta tashi a wani gini dake birnin Johannesburg, wadda kuma ta haddasa rasuwar mutane da dama.

Xi Jinping ya ce, a madadin gwamnatin Sin da jama’arta, yana jajantawa iyayen mamatan da bala’in ya ritsa da su. Ya ce, Sin na goyon bayan gwamnatin Afrika ta kudu da jama’arta. Ya kuma yi imanin cewa, a karkashin jagorancin Ramaphosa da gwamnatinsa, ba shakka jama’ar kasar za ta shawo kan wannan bala’in. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Zakarun turai

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.