ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Benin Da Kuma Aika Sakwanni Ga Takwarorinsa na Zimbabwe Da AFirka Ta Kudu

by CMG Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Da yammacin yau Juma’a ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya tattauna da takwaransa na kasar Benin Patrice Talon, wanda ke ziyarar aiki a nan birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka sanar da kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

Xi Jinping ya nuna cewa, Sin na goyon bayan nahiyar Afrika, a fannin zama wani muhimmin bangare na siyasa, da tattalin arziki, da al’adu a duniya, tana kuma mai fatan samar da sabbin damammaki bisa ci gaban da take samu, da kuma hadin kai da kasashen Afirka ciki har da Benin, don tabbatar da ci gaban da aka samu, a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afrika, da ingiza shawarar “ziri daya da hanya daya”, da shawarar raya duniya ta bai daya, da ma ajandar 2063 ta AU, da kuma tabbatar da tsare-tsaren bunkasuwar kasashen Afrika, har ma da goyon bayan kasashen nahiyar wajen samun farfadowar tattalin arziki, da bunkasuwa mai dorewa.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin

A nasa bangare, Patrice Talon cewa ya yi, shugabannin biyu sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwarsu a fannoni daban-daban, ciki har da zurfafa hadin kai wajen tabbatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da samun bunkasuwa, tare da kiyaye muhalli, da kayayyakin aikin gona, da kiwo lafiya da sauransu. Ban da wannan kuma, an gabatar da sanarwar kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

Sannan, a Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya takwaransa na kasar Zimbabwe Emmerson Dambudzo Mnangagwa, murnar zarcewa a mukamin shugaban kasa.

A sakon na sa ta wayar tarho, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, Sin da Zimbabwe na da hulda mai kyau. Kaza lika a shekarun baya-bayan nan, kasashen biyu na karfafa fahimtar juna a siyasance, tare da samun sakamako mai armashi a fannin hadin kai, da goyon bayan juna kan muradunsu masu tushe, a karkashin jagorancin shugabannin biyu.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Xi ya kara da cewa, Sin na dora muhimmanci matuka kan bunkasuwar huldar kasashen biyu, yana kuma mai fatan kara hadin kai da Emmerson Dambudzo Mnangagwa, a fannin ingiza samun sabon ci gaba, ta fuskar huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kiyaye adalci da daidaito na kasa da kasa, da muradun bai daya na kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, a yau Juma’a shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jajantawa takwaransa na kasar Afrika ta kudu Matamela Cyril Ramaphosa, bisa gobara da ta tashi a wani gini dake birnin Johannesburg, wadda kuma ta haddasa rasuwar mutane da dama.

Xi Jinping ya ce, a madadin gwamnatin Sin da jama’arta, yana jajantawa iyayen mamatan da bala’in ya ritsa da su. Ya ce, Sin na goyon bayan gwamnatin Afrika ta kudu da jama’arta. Ya kuma yi imanin cewa, a karkashin jagorancin Ramaphosa da gwamnatinsa, ba shakka jama’ar kasar za ta shawo kan wannan bala’in. (Amina Xu)

Xi Jinping
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Zakarun turai

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.