ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Benin Da Kuma Aika Sakwanni Ga Takwarorinsa na Zimbabwe Da AFirka Ta Kudu

by CMG Hausa
3 years ago
Xi Jinping

Da yammacin yau Juma’a ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya tattauna da takwaransa na kasar Benin Patrice Talon, wanda ke ziyarar aiki a nan birnin Beijing, inda bangarorin biyu suka sanar da kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

Xi Jinping ya nuna cewa, Sin na goyon bayan nahiyar Afrika, a fannin zama wani muhimmin bangare na siyasa, da tattalin arziki, da al’adu a duniya, tana kuma mai fatan samar da sabbin damammaki bisa ci gaban da take samu, da kuma hadin kai da kasashen Afirka ciki har da Benin, don tabbatar da ci gaban da aka samu, a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afrika, da ingiza shawarar “ziri daya da hanya daya”, da shawarar raya duniya ta bai daya, da ma ajandar 2063 ta AU, da kuma tabbatar da tsare-tsaren bunkasuwar kasashen Afrika, har ma da goyon bayan kasashen nahiyar wajen samun farfadowar tattalin arziki, da bunkasuwa mai dorewa.

  • Ana Zura Ido Kan Yadda Amurka Za Ta Ki Raba-gari Da Kasar Sin

A nasa bangare, Patrice Talon cewa ya yi, shugabannin biyu sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwarsu a fannoni daban-daban, ciki har da zurfafa hadin kai wajen tabbatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da samun bunkasuwa, tare da kiyaye muhalli, da kayayyakin aikin gona, da kiwo lafiya da sauransu. Ban da wannan kuma, an gabatar da sanarwar kafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu.

ADVERTISEMENT

Sannan, a Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya taya takwaransa na kasar Zimbabwe Emmerson Dambudzo Mnangagwa, murnar zarcewa a mukamin shugaban kasa.

A sakon na sa ta wayar tarho, shugaba Xi Jinping ya nuna cewa, Sin da Zimbabwe na da hulda mai kyau. Kaza lika a shekarun baya-bayan nan, kasashen biyu na karfafa fahimtar juna a siyasance, tare da samun sakamako mai armashi a fannin hadin kai, da goyon bayan juna kan muradunsu masu tushe, a karkashin jagorancin shugabannin biyu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Xi ya kara da cewa, Sin na dora muhimmanci matuka kan bunkasuwar huldar kasashen biyu, yana kuma mai fatan kara hadin kai da Emmerson Dambudzo Mnangagwa, a fannin ingiza samun sabon ci gaba, ta fuskar huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare, da kiyaye adalci da daidaito na kasa da kasa, da muradun bai daya na kasashe masu tasowa.

Bugu da kari, a yau Juma’a shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jajantawa takwaransa na kasar Afrika ta kudu Matamela Cyril Ramaphosa, bisa gobara da ta tashi a wani gini dake birnin Johannesburg, wadda kuma ta haddasa rasuwar mutane da dama.

Xi Jinping ya ce, a madadin gwamnatin Sin da jama’arta, yana jajantawa iyayen mamatan da bala’in ya ritsa da su. Ya ce, Sin na goyon bayan gwamnatin Afrika ta kudu da jama’arta. Ya kuma yi imanin cewa, a karkashin jagorancin Ramaphosa da gwamnatinsa, ba shakka jama’ar kasar za ta shawo kan wannan bala’in. (Amina Xu)

Xi Jinping
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Zakarun turai

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.