• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Da Shugaban Majalisar Zartaswar Turai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A safiyar yau Alhamis ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari tare da shugaban majalisar zartaswa ta Turai Charles Michel a babban dakin taruwar jama’a da ke birnin Beijing.

Xi Jinping ya bayyana cewa, dangantakar da ke tsakanin Sin da Turai ta dade da ci gaba, wadda ta dace da muradun bangarorin biyu da na kasashen duniya. Game da ci gaban dangantakar, Xi ya gabatar da ra’ayoyi guda hudu, na farko shi ne tabbatar da sanin juna yadda ya kamata, na biyu shi ne warware sabane-sabane yadda ya kamata, na uku shi ne inganta hadin kansu, sai na hudu kyautata daidaituwa a tsakanin kasa da kasa.

  • Xi Jinping Ya Aikawa MDD Sakon Murnar Taron Tunawa Da Ranar Goyon Bayan Palasdinawa

A jawabinsa Michel ya nuna cewa, Tarayyar Turai tana fatan zama abokiyar hadin gwiwar Sin ta kwarai.

A yayin tattaunawar bangarorin biyu kan matsalar Ukraine, Xi ya bayyana matsayin kasar Sin, yana mai cewa, warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa na dacewa da moriyar kasashen Asiya da Turai.

Sannan a wajen taron manema labarai da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta shirya a yau Alhamis, yayin da take amsa tambayar da ta shafi hadin-gwiwar Sin da Turai a fannin tattalin arziki da kasuwanci, mai magana da yawun ma’aikatar Shu Jueting ta bayyana cewa, kasarta na maida hankali sosai wajen bunkasa alakarta da kasashen Turai, da dukufa kan zurfafa hadin-gwiwarsu ta cimma moriyar juna, a wani kokari na tabbatar da samar da isassun kayayyaki a duniya, da kiyaye zaman doka da oda ta fuskar tattalin arziki da kasuwancin kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Rahotannin sun ce, a karkashin jagorancin shugabannin bangarorin biyu, akwai alakar tattalin arziki mai karfi tsakanin Sin da Turai a halin yanzu. Daga watan Janairu zuwa Oktobar bana, jimillar kudin cinikayyar su ta kai dala biliyan 711.4, adadin da ya karu da kaso 6.3 bisa dari. Kasar Sin ita ce babbar abokiyar cinikayya ta farko ga kungiyar tarayyar Turai wato EU, yayin da EU din ke ci gaba da zama babbar aminiyar cinikayya ta biyu ga kasar ta Sin. (Safiyah Ma, Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Soki Gwamnoni Kan Karkatar Da Kudaden Kananan Hukumomi

Next Post

Kungiyar Mata ‘Yan Jarida Ta Yi Sabuwar Shugaba A Kebbi

Related

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

7 hours ago
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

17 hours ago
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
Daga Birnin Sin

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

19 hours ago
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

20 hours ago
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

21 hours ago
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

22 hours ago
Next Post
Kungiyar Mata ‘Yan Jarida Ta Yi Sabuwar Shugaba A Kebbi

Kungiyar Mata 'Yan Jarida Ta Yi Sabuwar Shugaba A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi

August 7, 2025
Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don ÆŠaukar Nunez Daga Liverpool

Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don ÆŠaukar Nunez Daga Liverpool

August 7, 2025
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

August 7, 2025
Jami’an Tsaro Sun DaÆ™ile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun DaÆ™ile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin GurÉ“atattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin GurÉ“atattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.