• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Zai Fara Ziyararsa Ta Farko A Rasha Tun Da Aka Sake Zaben Sa A Matsayin Shugaban Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Zai Fara Ziyararsa Ta Farko A Rasha Tun Da Aka Sake Zaben Sa A Matsayin Shugaban Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa gayyatar da shugaba Vladimir Putin na Tarayyar Rasha ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyarar aiki kasar Rasha daga ranar 20 zuwa 22 ga watan Maris.

Wannan ita ce ziyara ta farko da Xi Jinping ya kai zuwa ketare tun bayan da aka sake zabar sa a matsayin shugaban kasar, kuma ziyara ce ta sada zumunci da tabbatar da hadin gwiwa da zaman lafiya, kana hanyar da za ta jagoranta da kuma tsara tsari kan dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Rasha a sabon zamani.

  • Ina Da Kwarin Guiwar Lashe Zaben Gwamnan Bauchi -Sanata Jika

Xi Jinping ya taba bayyana dangantakarsa da Putin a matsayin “alakar ra’ayin bai daya” kuma “ta aminci”. Shi ma a nasa bangaren shugaba Putin ya kira Xi Jinping “aboki nagari” kuma “aboki na aminci”. A watan Maris din shekarar 2013, lokacin da Xi Jinping, ya hau karagar mulkin kasar Sin karo na farko, ya zabi kasar Rasha a matsayin kasar da zai kai ziyararsa ta farko a kasashen waje.

Duk wani irin ci gaba da aka samu a cikin shekaru goma da suka gabata, kan dangantakar Sin da Rasha, ba za ta rasa nasaba da jagorancin shugabannin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare ba. A cikin wadannan shekaru goma kuma, Xi Jinping da Putin sun yi ganawa har sau 40. A karkashin jagorancin shugabannin kasashen biyu, Sin da Rasha sun yi nasarar shimfida hanyar amincewa da juna bisa manyan tsare-tsare a tsakanin manyan kasashen duniya, da yin mu’amalar sada zumunta tsakanin kasashen da ke makwabtaka, lamarin da ya zama abin koyi ga karfafa huldar kasa da kasa.

Wannan ziyarar da Xi Jinping zai kai kasar Rasha, shi ne karo na 9 da ya taka kafarsa a kasar Rasha tun bayan da ya hau kan karagar mulki. A kwanan baya, ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, a yayin wannan ziyara, Xi Jinping da Putin za su yi musayar ra’ayi mai zurfi kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da manyan batutuwan kasa da kasa da na shiyya-shiyya dake jawo hankulansu duka, kana da sa kaimi ga yin hakikanin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu, da kuma kaddamar da sabon kuzari ga ci gaban dangantakar kasashen biyu. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Labarai Masu Nasaba

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Inuwa Ya Samu Nasarar Tazarce A Kujerar Gwamna

Next Post

Farfesa Yoro Diallo: Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Tana Da Muhimmanci Matuka

Related

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

20 minutes ago
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya
Daga Birnin Sin

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

1 hour ago
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

3 hours ago
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

5 hours ago
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

23 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

1 day ago
Next Post
Farfesa Yoro Diallo: Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Tana Da Muhimmanci Matuka

Farfesa Yoro Diallo: Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Tana Da Muhimmanci Matuka

LABARAI MASU NASABA

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

He Lifeng Zai Ziyarci Birtaniya Tare Da Halartar Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka 

June 8, 2025
Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

Ndume Ya Gargaɗi Tinubu Kan 2027: “An Taɓa Yi Wa Jonathan Irin Wannan”

June 8, 2025
Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

Shugaban Xi Da Takwaransa Na Myanmar Sun Mikawa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 75 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya

June 8, 2025
Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

Kashim Shettima Ya Ƙaddamar Da Shirin Gyaran Kayayyakin Gwamnati A Borno

June 8, 2025
Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

Sin Na Kokarin Gina Yanayin Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa Da Kawance A Tekun Kudancin Kasar

June 8, 2025
Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Nemi Diyya Daga Gwamnatin Tarayya Kan Soke Hawan Sallah

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.