• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 16 ga wannan wata agogon kasar Peru, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa cibiyar taro ta Lima domin halartar kwarya-kwaryar taron shugabannin APEC karo na 31, tare da gabatar da wani muhimmin jawabi.

 

Cikin jawabinsa, Xi ya yi nuni da cewa, a halin yanzu, ana yin manyan sauye-sauye a duk fadin duniya, domin tattalin arzikin duniya bai samu ci gaba yadda ya kamata ba, kuma an gamu da matsala yayin bude kofa ga wasu, sannan hadin gwiwar dake tsakanin kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik shi ma yana fama da kalubale.

  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci
  • An Yi Bikin Kaddamar Da Shirin Zababbun Kalaman Shugaba Xi Jinping “Zango Na 3” Da Harshen Sifaniya A Peru

A don haka shugaban ya ce, ya dace kasashen yankin su hada kai domin tabbatar da muradun Putrajaya nan da shekarar 2040 da shugabannin APEC suka fitar a shekarar 2020, da karfafa gina kyakkyawar makomar bai daya ta al’ummun kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik, tare kuma da kafa sabon zamani na ci gaban yankin.

 

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Daga baya shugaba Xi ya gabatar da shawarwari uku, na farko, kafa tsarin hadin gwiwa ba tare da rufa-rufa ba tsakanin kasashen yankin. Ya ce, kasar Sin tana nacewa kan manufar aiwatar da tsare-tsaren RCEP, da CPTPP, da DEPA, haka nan tana son tattaunawa da bangarorin da abin ya shafa kan cinikayya a fannonin fasahar zamani da kare muhalli, tare kuma da kara habaka yankunan cinikayya marasa shinge zuwa matakin koli a fadin duniya.

 

Na biyu, neman samun sabon kuzarin kere-kere a yankin Asiya da tekun Fasifik, inda kasar Sin za ta fitar da “Shawarar hadin gwiwa kan musayar alkaluma tsakanin kasashen duniya”, domin zurfafa hadin gwiwa tsakaninta da sauran kasashen duniya a bangaren.

 

Na uku, tsara tunanin raya yankin Asiya da tekun Fasifik da zai haifar da alfanu ga kowa da kowa, yayin da a nata bangaren, kasar Sin za ta yi kokari domin kara kudin shigar al’ummun kasashen mambobin kungiyar APEC, da daukaka ci gaban matsakaita da kananan masana’antu, da habaka ci gaban tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasifik.

 

Ban da wannan kuma, Xi ya sanar da cewa, kasar Sin ce za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron da shugabannin kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta yankin Asiya da teku Fasifik APEC za su gudanar a shekarar 2026. Ya bayyana cewa, kasarsa tana maraba da kuma tsumayar aiki tare da dukkan bangarorin da abin ya shafa wajen zurfafa hadin gwiwar yankin Asiya da tekun Fasifik domin amfanar da al’ummomin manyan yankunan guda biyu. (Mai fassara: Jamila)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Me Nijeriya Za Ta Iya Amfana A Zaben Amurka?

Next Post

MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

51 minutes ago
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

22 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

23 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

24 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

1 day ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

1 day ago
Next Post
MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.