• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Halarci Kwarya-Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31 Tare Da Gabatar Da Jawabi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 16 ga wannan wata agogon kasar Peru, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa cibiyar taro ta Lima domin halartar kwarya-kwaryar taron shugabannin APEC karo na 31, tare da gabatar da wani muhimmin jawabi.

 

Cikin jawabinsa, Xi ya yi nuni da cewa, a halin yanzu, ana yin manyan sauye-sauye a duk fadin duniya, domin tattalin arzikin duniya bai samu ci gaba yadda ya kamata ba, kuma an gamu da matsala yayin bude kofa ga wasu, sannan hadin gwiwar dake tsakanin kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik shi ma yana fama da kalubale.

  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci
  • An Yi Bikin Kaddamar Da Shirin Zababbun Kalaman Shugaba Xi Jinping “Zango Na 3” Da Harshen Sifaniya A Peru

A don haka shugaban ya ce, ya dace kasashen yankin su hada kai domin tabbatar da muradun Putrajaya nan da shekarar 2040 da shugabannin APEC suka fitar a shekarar 2020, da karfafa gina kyakkyawar makomar bai daya ta al’ummun kasashen yankin Asiya da tekun Pasifik, tare kuma da kafa sabon zamani na ci gaban yankin.

 

Labarai Masu Nasaba

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Daga baya shugaba Xi ya gabatar da shawarwari uku, na farko, kafa tsarin hadin gwiwa ba tare da rufa-rufa ba tsakanin kasashen yankin. Ya ce, kasar Sin tana nacewa kan manufar aiwatar da tsare-tsaren RCEP, da CPTPP, da DEPA, haka nan tana son tattaunawa da bangarorin da abin ya shafa kan cinikayya a fannonin fasahar zamani da kare muhalli, tare kuma da kara habaka yankunan cinikayya marasa shinge zuwa matakin koli a fadin duniya.

 

Na biyu, neman samun sabon kuzarin kere-kere a yankin Asiya da tekun Fasifik, inda kasar Sin za ta fitar da “Shawarar hadin gwiwa kan musayar alkaluma tsakanin kasashen duniya”, domin zurfafa hadin gwiwa tsakaninta da sauran kasashen duniya a bangaren.

 

Na uku, tsara tunanin raya yankin Asiya da tekun Fasifik da zai haifar da alfanu ga kowa da kowa, yayin da a nata bangaren, kasar Sin za ta yi kokari domin kara kudin shigar al’ummun kasashen mambobin kungiyar APEC, da daukaka ci gaban matsakaita da kananan masana’antu, da habaka ci gaban tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasifik.

 

Ban da wannan kuma, Xi ya sanar da cewa, kasar Sin ce za ta karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron da shugabannin kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta yankin Asiya da teku Fasifik APEC za su gudanar a shekarar 2026. Ya bayyana cewa, kasarsa tana maraba da kuma tsumayar aiki tare da dukkan bangarorin da abin ya shafa wajen zurfafa hadin gwiwar yankin Asiya da tekun Fasifik domin amfanar da al’ummomin manyan yankunan guda biyu. (Mai fassara: Jamila)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Me Nijeriya Za Ta Iya Amfana A Zaben Amurka?

Next Post

MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

Related

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

12 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

13 hours ago
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping
Daga Birnin Sin

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

13 hours ago
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

14 hours ago
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

15 hours ago
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

16 hours ago
Next Post
MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.