A yau Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika wasikar taya murna ga Jami’ar Fudan, yayin da take murnar cika shekaru 120 da kafuwa.
Cikin wasikar taya murnar, Xi Jinping ya ce cikin sama da shekaru 120, Jami’ar Fudan ta yi ta tafiya da zamani da kuma daukaka akidar kishin kasa, ta kuma yi rainon dalibai masu hazaka da cimma nasarori na hakika da taka rawar gani a ci gaban kasar Sin.
- Mummunan Hatsarin Mota Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 19 A Kogi
- Akwai Alamar Tambaya A Sake Lalacewar Matatar Mai Ta Fatakwal A Karo Na 2, Bayan Kashe Dala Biliyan 1.5
Xi Jinping ya kuma bayyana fatan a wannan sabon mafari, Jami’ar Fudan za ta tsaya tsayin daka wajen amfani da ra’ayin gurguzu mai sigar kasar Sin a sabon zamani wajen samar da kwararru.
Ya kara da cewa ya kamata jami’ar ta zurfafa gyare-gyare a bangaren binciken ilimi da kimiyya da inganta kirkire-kirkiren kimiyya masu zaman kansu da samar da kuma ingiza kirkire-kirkire a bangarorin falsafa da kimiyyar zamantakewa.
Jami’ar Fudan da aka kafa a shekarar 1905 mai mazauni a birnin Shanghai, cikakkiyar jami’a ce dake mayar da hankali kan bincike. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp