Shugaban kasar Sin, Xi Jinping ya mika sakon taya murna a jiya Laraba ga Jean-Lucien Savi de Tove bisa karbar ragamar shugabancin kasar Togo.
Har ila yau, duk dai a ranar ta Laraba, Xi ya aike da sakon taya murna ga Faure Gnassingbe bisa kama aiki a matsayin shugaban majalisar ministocin Togo.
- Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025
- An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Xi ya ce, a ko da yaushe, kasashen biyu suna goyon bayan juna kan muhimman batutuwan da suka shafi moriyarsu da manyan abubuwan da ke ci musu tuwo a kwarya, kuma sun zama ababen koyi a bangaren daidaito a tsakanin kasashe ba tare da la’akari da yanayin girmansu ba, da kuma hadin kai da hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa.
Xi ya kara da cewa, yana mai da hankali sosai kan raya dangantakar da ke tsakanin Sin da Togo, kuma yana son yin aiki tare da shugabannin Togo wajen daukar aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na birnin Beijing, a matsayin wata dama ta ciyar da dadadden zumuncinsu gaba, da fadada hadin gwiwa a fannoni daban-daban, da ci gaba da kyautata ma’anar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, ta yadda za a amfanar da jama’ar kasashen biyu yadda ya kamata.
Kazalika, a ranar Larabar, firaministan kasar Sin, Li Qiang, ya aike da sakon taya murna ga Faure Gnassingbe bisa kama aiki a matsayin shugaban majalisar ministocin Togo. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp