Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sako ga Abdelmadjid Tebboune, inda ya taya shi murnar sake zabarsa da aka yi a matsayin shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyyar Algeria.
Xi Jinping ya bayyana cewa, yana jinjinawa ci gaban da aka samu a dangantakar Sin da Algeria, kuma a shirye yake ya hada hannu da shugaba Tebboune, wajen amfani da cikar dangantakar abota bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni tsakanin Sin da Algeria shekaru 10, a matsayin wata dama ta kara bunkasa aminci da fadadawa da zurfafa hadin gwiwarsu a aikace da hada hannu wajen kara damarmakin hadin gwiwar abota tsakanin kasashen biyu. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp