• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Kira Da A Inganta Fannin Noma Mai Sigar Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a ci gaba da kokarin inganta fannin aikin gona mai sigar musamman ta kasar Sin, a wani muhimmin taron ayyukan raya yankunan karkara, wanda aka gudanar daga ranar Jumma’a zuwa Asabar a birnin Beijing, babban birnin kasar Sin. 

Kasar Sin, mai yawan jama’a biliyan 1.4, wato kusan kashi 1 bisa 5 na al’ummar duniya, tana da kashi 9 cikin 100 na filayen noma a duniya. Mafi yawan abincin da ake samarwa daga gonakin kasar Sin ne.

  • Wang Yi Ya Yaba Da Ayyukan Diflomasiyyar Kasar Sin A Shekarar 2022

Bisa la’akari da karancin albarkatun da kasar ke da shi da kokarin kasar na samun kyakkyawar alaka tsakanin ‘yan Adam da muhalli, ya sa shugaba Xi ya bukaci daukar hanyar da ta dace da yanayin da kasar ke ciki, maimakon kwaikwayon kwarewa kai tsaye daga sauran kasashen dake da karfi a fannin aikin gona.

Taron na shekara-shekara wanda Xi ya jagoranta, ya samu halartar wakilan zaunannen kwamitin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin JKS. A yayin taron na yini biyu, shugaba Xi ya jaddada muhimmancin samun isasshen abinci, da samar da isassun kayayyakin amfanin gona a kasuwa, yana mai jaddada kiran farfado da yankunan karkara, wajen kara habaka kasuwanni da ci gaban kauyuka.

Xi ya bayyana cewa, kiyaye samun isasshen abinci, da tabbatar da samar da muhimman kayayyakin amfanin gona cikin aminci, su ne muhimman al’amurra na farko wajen karfafa fannin aikin gona na kasar Sin. Shugaba Xi, ya kuma bukaci da a sake yin wani sabon zagaye na inganta noman hatsi tare da daukar matakai masu tsauri.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

A yayin taron, Xi ya yi kira da a inganta filayen noma na asali na kasar zuwa filayen gonaki masu inganci akai-akai. Alkaluma na hukuma sun nuna cewa, nan da karshen shekarar 2022, filayen noman kasar masu inganci, za su kai kimanin kadada miliyan 66.67 (Ibrahim)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Next Post
Yadda Aka Kammala Shirin Kare Kasafin Kudi Na Ma’aikatun Gwamnatin Katsina

Yadda Aka Kammala Shirin Kare Kasafin Kudi Na Ma’aikatun Gwamnatin Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Xi

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.