• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Kira Da Dunkule Tattalin Arzikin Asia Da Pasifik Yayin Da Ake Fuskantar Kalubale

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Yi Kira Da Dunkule Tattalin Arzikin Asia Da Pasifik Yayin Da Ake Fuskantar Kalubale
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya bayyana a yau Alhamis cewa, yayin da ake fuskantar sabbin sauye-sauye, akwai bukatar mambobin kungiyar hadin gwiwar raya tattalin arzikin Asiya da Pasifik wato APEC, su yi waiwaye su dauki darasi daga tarihi, su tunkari kalubalen da ake fuskanta yanzu, tare da jajircewa wajen dunkule tattalin arzikin yankin Asia da Pasifik.

Xi Jinping wanda ya bayyana haka cikin rubutaccen jawabin ga taron kolin shugabannin masana’antu da kasuwanci na kungiyar APEC, ya yi kira da a hada hannu wajen samar da sabbin nasarori a fannin ci gaba da gina al’ummar Asia da Pasifik mai makoma ta bai daya.

  • Xi Jinping Ya Gana Da Babban Sakataren MDD

Ya kuma gabatar da wasu shawarwari 6 game da hakan, wadanda suka hada da, gina tubalin neman ci gaba cikin lumana da daukar dabarun neman ci gaba dake mayar da hankali kan moriyar jama’a da fadada bude kofa ga kasashen waje da jajircewa wajen hadewa da juna da gina nagartaccen tsarin samar da kayayyaki da kuma daukaka aikin raya tattalin arziki.

A cewar shugaba Xi, yankin Asiya da Pasifik ba wuri ne da kowa zai yi abun da ya ga dama ba, kuma bai kamata ya zamo dandalin takara ga manyan kasashe ba. Yana mai cewa, ba za a amince da duk wani yunkuri na tayar da wani yakin cacar baka a yankin ba.

Har ila yau, shugaban na kasar Sin ya bayyana cewa, bin tafarkin neman ci gaba cikin lumana, muhimmin zabi ne da kasarsa ta yi saboda muradun al’ummar Sinawa, kuma za su jajirce ga tabbatar da zaman lafiya da samun ci gaba da hadin gwiwa da samun moriyar juna.

Labarai Masu Nasaba

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Haka kuma, za su mayar da hankali ga kiyaye zaman lafiya da ci gaba a duniya, yayin da suke neman na su ci gaban, kana za su bayar da karin gudunmuwa ga zaman lafiyar duniya da ci gaba, ta hanyar na su ci gaban.

Da yake bayyana bude kofa da dunkulewa wuri guda a matsayin masu muhimmanci ga kwanciyar hankali da ci gaban bil Adama, Xi Jinping ya ce, daukacin al’ummar Asiya da Pasifik ne suka raya yankin ta hanyar hada hannu da shawo kan wahalhalu da kalubale.

Yana mai cewa, duk wani yunkuri na kawo tsaiko ko rusa tsarin samar da kayayyaki, da aka samar a yankin cikin shekaru da dama, babu abun da zai haifar face lalata hadin gwiwar raya tattalin arzikin yankin.

Ya ce bude kofa zai kawo ci gaba, yayin da rufewa za ta haifar da koma-baya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Za A Fara Shirye-shiryen Aikin Hajji Ranar 21 Ga Disamba – NAHCON

Next Post

Sake Fasalin Naira: Adadin Gwamnonin Da EFCC Ke Bibiya Na Sake Karuwa –Bawa

Related

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

1 hour ago
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

3 hours ago
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

4 hours ago
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

6 hours ago
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

7 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

1 day ago
Next Post
Sake Fasalin Naira: Adadin Gwamnonin Da EFCC Ke Bibiya Na Sake Karuwa –Bawa

Sake Fasalin Naira: Adadin Gwamnonin Da EFCC Ke Bibiya Na Sake Karuwa –Bawa

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.