• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Shawarwari Da Takwararsa Ta Peru

by Sulaiman and CGTN Hausa
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Yi Shawarwari Da Takwararsa Ta Peru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin jiya Alhamis 14 ga wannan wata agogon kasar Peru, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari da takwararsa ta kasar Peru Dina Boluarte, a fadar shugabar kasa dake birnin Lima, fadar mulkin kasar.

 

Yayin ganawarsu, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, tun bayan da kasarsa da kasar Peru suka daddale huldar diplomasiya shekaru 53 da suka gabata, an ci gaba da gudanar da huldar yadda ya kamata, musamman ma bayan da ya kai ziyarar aiki a karo na farko a kasar a shekarar 2016.

  • Xi Ya Sauka A Lima Na Peru Domin Halartar Kwarya Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31
  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA

A cikin wadannan shekaru, adadin cinikayya tsakanin kasashen biyu ya karu da ninki 1.6 karkashin kokarin da sassan biyu suka yi, kuma adadin jarin da kamfanonin kasar Sin suka zuba a Peru shi ma ya karu da ninki daya. Haka kuma kasashen biyu sun daga matsayin yarjejeniyar cinikayya maras shinge dake tsakaninsu. Duk wadannan suna haifar da matukar alfanu ga al’ummun kasashen biyu.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Kazalika, shugaba Xi ya ce Sin tana son yin kokari tare da bangaren Peru, wajen ingiza ci gaban huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare daga duk fannoni zuwa wani sabon mataki, tare kuma da samar da karin alfanu ga al’ummun sassan biyu.

 

Hakazalika, shugaba Xi da shugaba Boluarte, sun halarci bikin kaddamar da tashar ruwa ta Chancay ta Peru a birnin Lima ta kafar bidiyo tare. Tashar ruwa ta Chancay tana hade ne da gabar tekun Chancay mai nisan kusan kilomita 80 daga arewacin Lima, kuma muhimmin aiki ne da kasashen Sin da Peru suka gina tare bisa shawarar ziri daya da hanya daya, kana tashar ruwa ta zamani irinta ta farko dake yankin Latin Amurka, wadda za ta kasance sabuwar tashar ruwa mai muhimmanci a yankin Latin Amurka da tekun Pasifik.

 

Bayan kammala kaso na farko na aikin gininta, za ta taimaka wajen rage lokacin jigilar kayayyaki daga Peru zuwa kasar Sin ta jiragen ruwan dakon kaya zuwa kwanaki 23 kacal, kuma hakan zai haifar da tsimin kudin da za a kashe a bangaren da kaso 20 bisa dari, tare da bunkasa kudin shiga ga Peru da yawansu zai kai dalar Amurka biliyan 4.5, tare kuma da samar da guraben aikin yi na kai tsaye har sama da 8000 ga al’ummun kasar Peru. (Mai fassara: Jamila)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Sauka A Lima Na Peru Domin Halartar Kwarya Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31

Next Post

Kamfanonin Wayoyin Sadarwa Na Kasar Sin Na Fatan Fadada Kasuwanninsu A Nahiyar Afirka

Related

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

46 minutes ago
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
Daga Birnin Sin

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

21 hours ago
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan
Daga Birnin Sin

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

22 hours ago
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
Daga Birnin Sin

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

23 hours ago
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

24 hours ago
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

1 day ago
Next Post
Kamfanonin Wayoyin Sadarwa Na Kasar Sin Na Fatan Fadada Kasuwanninsu A Nahiyar Afirka

Kamfanonin Wayoyin Sadarwa Na Kasar Sin Na Fatan Fadada Kasuwanninsu A Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

August 8, 2025
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

August 8, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

August 8, 2025
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

August 8, 2025
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

August 8, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.