• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Shawarwari Da Takwararsa Ta Peru

by Sulaiman and CGTN Hausa
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Yi Shawarwari Da Takwararsa Ta Peru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin jiya Alhamis 14 ga wannan wata agogon kasar Peru, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari da takwararsa ta kasar Peru Dina Boluarte, a fadar shugabar kasa dake birnin Lima, fadar mulkin kasar.

 

Yayin ganawarsu, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, tun bayan da kasarsa da kasar Peru suka daddale huldar diplomasiya shekaru 53 da suka gabata, an ci gaba da gudanar da huldar yadda ya kamata, musamman ma bayan da ya kai ziyarar aiki a karo na farko a kasar a shekarar 2016.

  • Xi Ya Sauka A Lima Na Peru Domin Halartar Kwarya Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31
  • Cire Tallafin Man Fetur Ya Kawo Ƙarshen Fasa-ƙwauri, in ji NSA

A cikin wadannan shekaru, adadin cinikayya tsakanin kasashen biyu ya karu da ninki 1.6 karkashin kokarin da sassan biyu suka yi, kuma adadin jarin da kamfanonin kasar Sin suka zuba a Peru shi ma ya karu da ninki daya. Haka kuma kasashen biyu sun daga matsayin yarjejeniyar cinikayya maras shinge dake tsakaninsu. Duk wadannan suna haifar da matukar alfanu ga al’ummun kasashen biyu.

 

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Kazalika, shugaba Xi ya ce Sin tana son yin kokari tare da bangaren Peru, wajen ingiza ci gaban huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare daga duk fannoni zuwa wani sabon mataki, tare kuma da samar da karin alfanu ga al’ummun sassan biyu.

 

Hakazalika, shugaba Xi da shugaba Boluarte, sun halarci bikin kaddamar da tashar ruwa ta Chancay ta Peru a birnin Lima ta kafar bidiyo tare. Tashar ruwa ta Chancay tana hade ne da gabar tekun Chancay mai nisan kusan kilomita 80 daga arewacin Lima, kuma muhimmin aiki ne da kasashen Sin da Peru suka gina tare bisa shawarar ziri daya da hanya daya, kana tashar ruwa ta zamani irinta ta farko dake yankin Latin Amurka, wadda za ta kasance sabuwar tashar ruwa mai muhimmanci a yankin Latin Amurka da tekun Pasifik.

 

Bayan kammala kaso na farko na aikin gininta, za ta taimaka wajen rage lokacin jigilar kayayyaki daga Peru zuwa kasar Sin ta jiragen ruwan dakon kaya zuwa kwanaki 23 kacal, kuma hakan zai haifar da tsimin kudin da za a kashe a bangaren da kaso 20 bisa dari, tare da bunkasa kudin shiga ga Peru da yawansu zai kai dalar Amurka biliyan 4.5, tare kuma da samar da guraben aikin yi na kai tsaye har sama da 8000 ga al’ummun kasar Peru. (Mai fassara: Jamila)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Sauka A Lima Na Peru Domin Halartar Kwarya Kwaryar Taron Shugabannin APEC Karo Na 31

Next Post

Kamfanonin Wayoyin Sadarwa Na Kasar Sin Na Fatan Fadada Kasuwanninsu A Nahiyar Afirka

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

5 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

7 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

7 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

11 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

13 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

13 hours ago
Next Post
Kamfanonin Wayoyin Sadarwa Na Kasar Sin Na Fatan Fadada Kasuwanninsu A Nahiyar Afirka

Kamfanonin Wayoyin Sadarwa Na Kasar Sin Na Fatan Fadada Kasuwanninsu A Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.